Home DUNIYA Sojojin dake Mulki a Kasar Mali Sun Mayar da Rundunar ‘Yan Sandan...

Sojojin dake Mulki a Kasar Mali Sun Mayar da Rundunar ‘Yan Sandan Kasar Karkashin SU

Gwamnatin mulkin Sojin Mali ta mayar da ‘yan sandan kasar karkashin rundunar sojojinta, a kokarin da take yi na murkushe ‘yan ‘ta’adda masu ikirarin Jihadi, wadanda suka shafe shekaru akalla 10 suna addabar sassan kasar.

Gwamnatin sojin kasar ta Mali ta ce matakin zai ba ta damar jibge ‘yan sandan a yankunan da sojoji suka kwato daga hannun ‘yan ta’adda, domin tabbatar da tsaron jama’a da dukiyarsu, da kuma dakile duk wani yunkuri na masu ikirarin jihadi ko ‘yan tawaye sake mamaye yankunan da suka subuce musu.

Majalisar zartaswar kasar ta rikon kwarya ce kuma ta CNT wadda sojojin da suka yi juyin mulki suka kafa ta zartar da dokar baiwa jami’an tsaro na ‘yan sanda kayan aikin sojoji mako guda da ya gabata.

Sai dai tun kafin amincewa da aiwatar da matakin mayar da su karkashin rundunar sojoji kungiyoyin ‘yan sandan suka soki manufar da suka bayyana a matsayin shawarar da bangare daya yayi gaban kansa wajen zartaswa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp