Home Labarai Yanzu-yanzu: Gwamnatin Tarayya Nijeriya tayi watsi da shirin CBN na sauya fasalin...

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Tarayya Nijeriya tayi watsi da shirin CBN na sauya fasalin kudin Kasar.

Bayan Sa’oi 48 da Gwamnan babban bankin Nijeriya CBN, Godwin Emefiele ya sanar da kudirin sa na sauya fasalin kudin kasar, nan da 15 ga watan Disambar 2022, Gwamnatin tarayyar kasar ta barranta kanta da yunkurin nasa.

Ministar kudi kasafi da tsare-tsare Hajiya Zainab Ahmad ce ta bayyana hakan, inda tace sauya fasalin kudin ka iya haifar da gagarumin tasgaro ga Kasar dama tattalin arzikin kasar.

yayin da take amsa tambayoyi a wurin kare kasafin kudin ma’akatar ta  gaban majalisar bayan da sanata Opeyemi Bamidele ya tambaye ta inda ta gargadi CBN kan abinda kaje kazo kan lamarin sauya fasalin kudin.

Sanata Bamidele yayi tambayan ko mene yasa kwanaki biyu bayan bayyana kudin sauya fasalin kudin dalar Amurka ta tashi daga 740 zuwa 788 sakamakon rige-rigen da ake na sauya kudin zuwa dalar Amurka.

https://timesng.com/naira-black-market-exchange-rate-today/

Idan za’a iya tunawa a ranar Laraba Gwamnan Babban Bankin na CBN  Emefiele bankin zai sauya fasalin takardun kudin kasar daga naira 200 har zuwa 1000.

Emefiele yace an dauki wannan mataki ne kasancewar yadda ake tasarrufi da kudaden kuma CBN bazai bari ake mu’amala da kudin taci-barkatai ba.

Yace sun dogara ne da sashe na 19 karamin kashi na A da B na dokar babban bankin ta shekarar 2007, wadda ta baiwa hukumar bankin dama bisa sahalewar shugaba Muhammadu Buhari su sauya fasalin kudin kasar daga kan 200 zuwa 1000.

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Tarayya Nijeriya tayi watsi da shirin CBN na sauya fasalin kudin Kasar.

Bayan Sa’oi 48 da Gwamnan babban bankin Nijeriya CBN, Godwin Emefiele ya sanar da kudirin sa na sauya fasalin kudin kasar nan da 15 ga watan Disambar 2022, Gwamnatin tarayyar kasar ta barranta kanta da yunkurin.

Ministar kudi kasafi da tsare-tsare Hajiya Zainab Ahmad ce ta bayyana hakan, inda tace sauya fasalin kudin ka iya haifar da gagarumin tasgaro ga Kasar dama tattalin arzikin kasar.

yayin da take amsa tambayoyi a wurin kare kasafin kudin ma’akatar ta  gaban majalisar bayan da sanata Opeyemi Bamidele ya tambaye ta inda ta gargadi CBN kan abinda kaje kazo kan lamarin sauya fasalin kudin.

Sanata Bamidele yayi tambayan ko mene yasa kwanaki biyu bayan bayyana kudin sauya fasalin kudin dalar Amurka ta tashi daga 740 zuwa 788 sakamakon rige-rigen da ake na sauya kudin zuwa dalar Amurka.

Idan za’a iya tunawa a ranar Laraba Gwamnan Babban Bankin na CBN  Emefiele bankin zai sauya fasalin takardun kudin kasar daga naira 200 har zuwa 1000.

Emefiele yace an dauki wannan mataki ne kasancewar yadda ake tasarrufi da kudaden kuma CBN bazai bari ake mu’amala da kudin taci-barkatai ba.

Yace sun dogara ne da sashe na 19 karamin kashi na A da B na dokar babban bankin ta shekarar 2007, wadda ta baiwa hukumar bankin dama bisa sahalewar shugaba Muhammadu Buhari su sauya fasalin kudin kasar daga kan 200 zuwa 1000.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp