Home Labarai Yanzu-yanzu: Gwamnatin Tarayya Nijeriya tayi watsi da shirin CBN na sauya fasalin...

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Tarayya Nijeriya tayi watsi da shirin CBN na sauya fasalin kudin Kasar.

Bayan Sa’oi 48 da Gwamnan babban bankin Nijeriya CBN, Godwin Emefiele ya sanar da kudirin sa na sauya fasalin kudin kasar, nan da 15 ga watan Disambar 2022, Gwamnatin tarayyar kasar ta barranta kanta da yunkurin nasa.

Ministar kudi kasafi da tsare-tsare Hajiya Zainab Ahmad ce ta bayyana hakan, inda tace sauya fasalin kudin ka iya haifar da gagarumin tasgaro ga Kasar dama tattalin arzikin kasar.

yayin da take amsa tambayoyi a wurin kare kasafin kudin ma’akatar ta  gaban majalisar bayan da sanata Opeyemi Bamidele ya tambaye ta inda ta gargadi CBN kan abinda kaje kazo kan lamarin sauya fasalin kudin.

Sanata Bamidele yayi tambayan ko mene yasa kwanaki biyu bayan bayyana kudin sauya fasalin kudin dalar Amurka ta tashi daga 740 zuwa 788 sakamakon rige-rigen da ake na sauya kudin zuwa dalar Amurka.

https://timesng.com/naira-black-market-exchange-rate-today/

Idan za’a iya tunawa a ranar Laraba Gwamnan Babban Bankin na CBN  Emefiele bankin zai sauya fasalin takardun kudin kasar daga naira 200 har zuwa 1000.

Emefiele yace an dauki wannan mataki ne kasancewar yadda ake tasarrufi da kudaden kuma CBN bazai bari ake mu’amala da kudin taci-barkatai ba.

Yace sun dogara ne da sashe na 19 karamin kashi na A da B na dokar babban bankin ta shekarar 2007, wadda ta baiwa hukumar bankin dama bisa sahalewar shugaba Muhammadu Buhari su sauya fasalin kudin kasar daga kan 200 zuwa 1000.

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Tarayya Nijeriya tayi watsi da shirin CBN na sauya fasalin kudin Kasar.

Bayan Sa’oi 48 da Gwamnan babban bankin Nijeriya CBN, Godwin Emefiele ya sanar da kudirin sa na sauya fasalin kudin kasar nan da 15 ga watan Disambar 2022, Gwamnatin tarayyar kasar ta barranta kanta da yunkurin.

Ministar kudi kasafi da tsare-tsare Hajiya Zainab Ahmad ce ta bayyana hakan, inda tace sauya fasalin kudin ka iya haifar da gagarumin tasgaro ga Kasar dama tattalin arzikin kasar.

yayin da take amsa tambayoyi a wurin kare kasafin kudin ma’akatar ta  gaban majalisar bayan da sanata Opeyemi Bamidele ya tambaye ta inda ta gargadi CBN kan abinda kaje kazo kan lamarin sauya fasalin kudin.

Sanata Bamidele yayi tambayan ko mene yasa kwanaki biyu bayan bayyana kudin sauya fasalin kudin dalar Amurka ta tashi daga 740 zuwa 788 sakamakon rige-rigen da ake na sauya kudin zuwa dalar Amurka.

Idan za’a iya tunawa a ranar Laraba Gwamnan Babban Bankin na CBN  Emefiele bankin zai sauya fasalin takardun kudin kasar daga naira 200 har zuwa 1000.

Emefiele yace an dauki wannan mataki ne kasancewar yadda ake tasarrufi da kudaden kuma CBN bazai bari ake mu’amala da kudin taci-barkatai ba.

Yace sun dogara ne da sashe na 19 karamin kashi na A da B na dokar babban bankin ta shekarar 2007, wadda ta baiwa hukumar bankin dama bisa sahalewar shugaba Muhammadu Buhari su sauya fasalin kudin kasar daga kan 200 zuwa 1000.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp