Home Labarai Yanzu-yanzu: Gwamnatin Tarayya Nijeriya tayi watsi da shirin CBN na sauya fasalin...

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Tarayya Nijeriya tayi watsi da shirin CBN na sauya fasalin kudin Kasar.

Bayan Sa’oi 48 da Gwamnan babban bankin Nijeriya CBN, Godwin Emefiele ya sanar da kudirin sa na sauya fasalin kudin kasar, nan da 15 ga watan Disambar 2022, Gwamnatin tarayyar kasar ta barranta kanta da yunkurin nasa.

Ministar kudi kasafi da tsare-tsare Hajiya Zainab Ahmad ce ta bayyana hakan, inda tace sauya fasalin kudin ka iya haifar da gagarumin tasgaro ga Kasar dama tattalin arzikin kasar.

yayin da take amsa tambayoyi a wurin kare kasafin kudin ma’akatar ta  gaban majalisar bayan da sanata Opeyemi Bamidele ya tambaye ta inda ta gargadi CBN kan abinda kaje kazo kan lamarin sauya fasalin kudin.

Sanata Bamidele yayi tambayan ko mene yasa kwanaki biyu bayan bayyana kudin sauya fasalin kudin dalar Amurka ta tashi daga 740 zuwa 788 sakamakon rige-rigen da ake na sauya kudin zuwa dalar Amurka.

https://timesng.com/naira-black-market-exchange-rate-today/

Idan za’a iya tunawa a ranar Laraba Gwamnan Babban Bankin na CBN  Emefiele bankin zai sauya fasalin takardun kudin kasar daga naira 200 har zuwa 1000.

Emefiele yace an dauki wannan mataki ne kasancewar yadda ake tasarrufi da kudaden kuma CBN bazai bari ake mu’amala da kudin taci-barkatai ba.

Yace sun dogara ne da sashe na 19 karamin kashi na A da B na dokar babban bankin ta shekarar 2007, wadda ta baiwa hukumar bankin dama bisa sahalewar shugaba Muhammadu Buhari su sauya fasalin kudin kasar daga kan 200 zuwa 1000.

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Tarayya Nijeriya tayi watsi da shirin CBN na sauya fasalin kudin Kasar.

Bayan Sa’oi 48 da Gwamnan babban bankin Nijeriya CBN, Godwin Emefiele ya sanar da kudirin sa na sauya fasalin kudin kasar nan da 15 ga watan Disambar 2022, Gwamnatin tarayyar kasar ta barranta kanta da yunkurin.

Ministar kudi kasafi da tsare-tsare Hajiya Zainab Ahmad ce ta bayyana hakan, inda tace sauya fasalin kudin ka iya haifar da gagarumin tasgaro ga Kasar dama tattalin arzikin kasar.

yayin da take amsa tambayoyi a wurin kare kasafin kudin ma’akatar ta  gaban majalisar bayan da sanata Opeyemi Bamidele ya tambaye ta inda ta gargadi CBN kan abinda kaje kazo kan lamarin sauya fasalin kudin.

Sanata Bamidele yayi tambayan ko mene yasa kwanaki biyu bayan bayyana kudin sauya fasalin kudin dalar Amurka ta tashi daga 740 zuwa 788 sakamakon rige-rigen da ake na sauya kudin zuwa dalar Amurka.

Idan za’a iya tunawa a ranar Laraba Gwamnan Babban Bankin na CBN  Emefiele bankin zai sauya fasalin takardun kudin kasar daga naira 200 har zuwa 1000.

Emefiele yace an dauki wannan mataki ne kasancewar yadda ake tasarrufi da kudaden kuma CBN bazai bari ake mu’amala da kudin taci-barkatai ba.

Yace sun dogara ne da sashe na 19 karamin kashi na A da B na dokar babban bankin ta shekarar 2007, wadda ta baiwa hukumar bankin dama bisa sahalewar shugaba Muhammadu Buhari su sauya fasalin kudin kasar daga kan 200 zuwa 1000.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp