Home DUNIYA Ana Cigaba da Aikin Ceton Wadanda Gada ta Rufta Dasu a Kasar...

Ana Cigaba da Aikin Ceton Wadanda Gada ta Rufta Dasu a Kasar India

Rahotanni na bayyana cewa ana cigaba da laluben wadanda suka nutse a ruwa bayan ruftawar wata tsohuwar gada a kasar India, abinda ake ganin ya shafi akalla mutane 130.

Tun da fari dai ‘Yan sanda a kasar sun tabbatar da mutuwar mutane fiye da 130, lokacin da wata gada da ta kwashe shekaru sama da 100 ana amfani da ita ta rushe, abinda ya sanya wasu da dama  fadawa ruwa.

Daya daga cikin manyan jami’an ‘yan sanda a kasar ta India, Ashok Kumar Yadav, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewar zuwa wayewar garin Litinin din nan, adadin mutane 132 aka tabbatar da mutuwarsu bayan rushewar gadar da ta kwashe kusan shekaru 150 ana amfani da ita.

Ministan dake kula da Yammacin jihar Gujerat, Brijesh Merja yace kuma anyi nasarar ceto mutane sama da 80 da ransu.

Mahukunta sun ce akalla mutane kusan 500 ke kan gadar lokacin da ta rufta sakamakon sakewar da robobin dake rike da ita suka yi, cikin su harda mata da yara.

Ita dai wannan gadar ba’a dade da kammala gyaranta ba, tana garin Morbi ne dake da nisan kilomita 200 daga Ahmedabad a Jihar Yammacin Gujerat.

Kafofin yada labaran kasar sun ce mutanen da suka taru akan gadar suna gudanar da ibada ne akan kogin Machchhu, yayin da wasu kafofi suka nuna hotunan bidiyon da ake bayyana cewar na hadarin ne dauke da mutanen dake kokarin yin fito domin tsira da rayukansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp