Home DUNIYA Ana Cigaba da Aikin Ceton Wadanda Gada ta Rufta Dasu a Kasar...

Ana Cigaba da Aikin Ceton Wadanda Gada ta Rufta Dasu a Kasar India

Rahotanni na bayyana cewa ana cigaba da laluben wadanda suka nutse a ruwa bayan ruftawar wata tsohuwar gada a kasar India, abinda ake ganin ya shafi akalla mutane 130.

Tun da fari dai ‘Yan sanda a kasar sun tabbatar da mutuwar mutane fiye da 130, lokacin da wata gada da ta kwashe shekaru sama da 100 ana amfani da ita ta rushe, abinda ya sanya wasu da dama  fadawa ruwa.

Daya daga cikin manyan jami’an ‘yan sanda a kasar ta India, Ashok Kumar Yadav, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewar zuwa wayewar garin Litinin din nan, adadin mutane 132 aka tabbatar da mutuwarsu bayan rushewar gadar da ta kwashe kusan shekaru 150 ana amfani da ita.

Ministan dake kula da Yammacin jihar Gujerat, Brijesh Merja yace kuma anyi nasarar ceto mutane sama da 80 da ransu.

Mahukunta sun ce akalla mutane kusan 500 ke kan gadar lokacin da ta rufta sakamakon sakewar da robobin dake rike da ita suka yi, cikin su harda mata da yara.

Ita dai wannan gadar ba’a dade da kammala gyaranta ba, tana garin Morbi ne dake da nisan kilomita 200 daga Ahmedabad a Jihar Yammacin Gujerat.

Kafofin yada labaran kasar sun ce mutanen da suka taru akan gadar suna gudanar da ibada ne akan kogin Machchhu, yayin da wasu kafofi suka nuna hotunan bidiyon da ake bayyana cewar na hadarin ne dauke da mutanen dake kokarin yin fito domin tsira da rayukansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp