Home Labarai ‘Yan Bindiga sun Sace Matafiya a Yankin Ekiti

‘Yan Bindiga sun Sace Matafiya a Yankin Ekiti

‘Yan Bindiga sun Sace Matafiya a Yankin Ekiti

 

Wasu ‘yan bindiga kimanin bakwai sun kai hari a kan titin Irele Ekiti, a karamar hukumar Ajoni da ke jihar Ekiti, inda suka yi awon gaba da matafiya hudu zuwa inda ba a san inda suke ba.

Majiyoyi sun ce matafiya hudun na kan hanyar zuwa birnin Ibadan na jihar Oyo ne da misalin karfe 11 na safiyar ranar Lahadi daga jihar Kogi inda suka halarci wani taron da lamarin ya faru.

Majiyar ta ce masu garkuwa da mutane dauke da bindigu sun bindige matafiyan ne a kofar Irele Ekiti da ke karshen Irele-OkeAko na hanyar inda suka garzaya da su dajin.

Wata majiya ta ce a ranar Litinin, “Ba mu ji komai daga bakin ‘yan bindigar ba tun ranar Lahadi. Muna fatan za su tuntubi iyalansu domin neman kudin fansa.”

Wani shugaban al’ummar Irele-Ekiti, wanda ya bayyana sunansa da Kehinde, ya tabbatar da sace shi.

Ya koka da yadda ‘yan bindiga ke kai hare-hare a yankin, inda ya yi kira ga gwamnati da ta kara kaimi wajen tabbatar da tsaro a yankin.

Kehinde ya bukaci gwamnan jihar Ekiti, Biodun Oyebanji, da ya ja hankalin sojoji da su samar da sansanin tsaro da za su kare yankin daga ‘yan bindigar da suka addabi yankin.

Kwamandan rundunar na Amotekun, Birgediya Janar Joe Komolafe (mai ritaya), wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce, “Rundunar jami’an tsaron na toshe dajin da ke yankin domin kubutar da wadanda lamarin ya rutsa da su tare da damke masu laifin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp