Home DUNIYA An Yiwa ‘Yan Jaridu 117 Kisan Gilla a Bakin Aikinsu daga 2020...

An Yiwa ‘Yan Jaridu 117 Kisan Gilla a Bakin Aikinsu daga 2020 zuwa 2021

Hukumar kula da ilimi, kimiyya al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya UNESCO ta koka da yadda wani bincike ke nuna cewa kaso mai yawa na wadanda ke kashe ‘yan jaridu basa fuskantar hukunci kana bin da suka aikata.

Wannan na zuwa ne daidai lokacin da Duniya ke bikin ranar kare hakkin ’yan jaridu, inda ta cikin rahoton da UNESCO ta fitar yau laraba, ta ce matsalar kisan ‘yan jaridu ta kai kololuwa a halin da ake ciki, yayinda kashi 86 na wadanda suka aikata kisan basa fuskantar hukunci.

Gabanin fitar da rahoton na yau, UNESCO a wani taron manema labarai da ta kira kan  barazanar da ‘yan jaridu ke fuskanta a sassan Duniya, ta bukaci daukar matakan baiwa ‘yan jaridun kariya la’akari da sadaukarwar da suke yi.

Rahoton na UNESCO ya ce wajibi daukar matakan gudanar da bincike tare da tabbatar da ganin an hukunta wadanda ke da hannu a cin zarafi ko kuma kisan ‘yan jaridu.

A cewar hukumar, halin da ‘yan jaridu ke ciki musamman a yankunan da ake fama da yaki ko kuma matsalolin tsaro baa bin yadda ba ne kuma ya na bukatar daukar matakan magancewa.

Manufar ranar ta yau na da nufin kare hakkin ‘yan jaridu tare da kawo karshen tsangwama ko kyara ko kuma cin zarafin da suke fuskanta a bakin aikinsu lamarin da UNESCO ta ce dole a samar da cikakkiyar kariya ga ‘yan jaridar.

Darakta Janar ta hukumar UNESCO Audrey Azoulay ta ce idan har ba a baiwa ‘yan jaridun kariyar da ta kamata ba, kenan za a dankwafar da hakkin fadar albarkacin baki.

Rahoton na UNESCO ya ce tsakanin shekarar 2020 zuwa 2021 an yiwa ‘yan jaridu 117 kisan gilla lokacin da suke bakin aikinsu, yayinda wasu 91 kuma aka kashe ba a bakin aiki ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp