Home DUNIYA An Yiwa ‘Yan Jaridu 117 Kisan Gilla a Bakin Aikinsu daga 2020...

An Yiwa ‘Yan Jaridu 117 Kisan Gilla a Bakin Aikinsu daga 2020 zuwa 2021

Hukumar kula da ilimi, kimiyya al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya UNESCO ta koka da yadda wani bincike ke nuna cewa kaso mai yawa na wadanda ke kashe ‘yan jaridu basa fuskantar hukunci kana bin da suka aikata.

Wannan na zuwa ne daidai lokacin da Duniya ke bikin ranar kare hakkin ’yan jaridu, inda ta cikin rahoton da UNESCO ta fitar yau laraba, ta ce matsalar kisan ‘yan jaridu ta kai kololuwa a halin da ake ciki, yayinda kashi 86 na wadanda suka aikata kisan basa fuskantar hukunci.

Gabanin fitar da rahoton na yau, UNESCO a wani taron manema labarai da ta kira kan  barazanar da ‘yan jaridu ke fuskanta a sassan Duniya, ta bukaci daukar matakan baiwa ‘yan jaridun kariya la’akari da sadaukarwar da suke yi.

Rahoton na UNESCO ya ce wajibi daukar matakan gudanar da bincike tare da tabbatar da ganin an hukunta wadanda ke da hannu a cin zarafi ko kuma kisan ‘yan jaridu.

A cewar hukumar, halin da ‘yan jaridu ke ciki musamman a yankunan da ake fama da yaki ko kuma matsalolin tsaro baa bin yadda ba ne kuma ya na bukatar daukar matakan magancewa.

Manufar ranar ta yau na da nufin kare hakkin ‘yan jaridu tare da kawo karshen tsangwama ko kyara ko kuma cin zarafin da suke fuskanta a bakin aikinsu lamarin da UNESCO ta ce dole a samar da cikakkiyar kariya ga ‘yan jaridar.

Darakta Janar ta hukumar UNESCO Audrey Azoulay ta ce idan har ba a baiwa ‘yan jaridun kariyar da ta kamata ba, kenan za a dankwafar da hakkin fadar albarkacin baki.

Rahoton na UNESCO ya ce tsakanin shekarar 2020 zuwa 2021 an yiwa ‘yan jaridu 117 kisan gilla lokacin da suke bakin aikinsu, yayinda wasu 91 kuma aka kashe ba a bakin aiki ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp