Home DUNIYA An Yiwa ‘Yan Jaridu 117 Kisan Gilla a Bakin Aikinsu daga 2020...

An Yiwa ‘Yan Jaridu 117 Kisan Gilla a Bakin Aikinsu daga 2020 zuwa 2021

Hukumar kula da ilimi, kimiyya al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya UNESCO ta koka da yadda wani bincike ke nuna cewa kaso mai yawa na wadanda ke kashe ‘yan jaridu basa fuskantar hukunci kana bin da suka aikata.

Wannan na zuwa ne daidai lokacin da Duniya ke bikin ranar kare hakkin ’yan jaridu, inda ta cikin rahoton da UNESCO ta fitar yau laraba, ta ce matsalar kisan ‘yan jaridu ta kai kololuwa a halin da ake ciki, yayinda kashi 86 na wadanda suka aikata kisan basa fuskantar hukunci.

Gabanin fitar da rahoton na yau, UNESCO a wani taron manema labarai da ta kira kan  barazanar da ‘yan jaridu ke fuskanta a sassan Duniya, ta bukaci daukar matakan baiwa ‘yan jaridun kariya la’akari da sadaukarwar da suke yi.

Rahoton na UNESCO ya ce wajibi daukar matakan gudanar da bincike tare da tabbatar da ganin an hukunta wadanda ke da hannu a cin zarafi ko kuma kisan ‘yan jaridu.

A cewar hukumar, halin da ‘yan jaridu ke ciki musamman a yankunan da ake fama da yaki ko kuma matsalolin tsaro baa bin yadda ba ne kuma ya na bukatar daukar matakan magancewa.

Manufar ranar ta yau na da nufin kare hakkin ‘yan jaridu tare da kawo karshen tsangwama ko kyara ko kuma cin zarafin da suke fuskanta a bakin aikinsu lamarin da UNESCO ta ce dole a samar da cikakkiyar kariya ga ‘yan jaridar.

Darakta Janar ta hukumar UNESCO Audrey Azoulay ta ce idan har ba a baiwa ‘yan jaridun kariyar da ta kamata ba, kenan za a dankwafar da hakkin fadar albarkacin baki.

Rahoton na UNESCO ya ce tsakanin shekarar 2020 zuwa 2021 an yiwa ‘yan jaridu 117 kisan gilla lokacin da suke bakin aikinsu, yayinda wasu 91 kuma aka kashe ba a bakin aiki ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp