Home Labarai Kalaman Nuna Gazawar Ministan Ilimin Nijeriya sun bar baya da Kura

Kalaman Nuna Gazawar Ministan Ilimin Nijeriya sun bar baya da Kura

Kalaman ministan ilimin Nijeriya Adamu Adamu na cigaba da yamutsa hazo a kasar, inda wa suke ganin cewa kamata yayi ace ya ajje mukamin tun da fari daya fahimci gazawar tasa.

Tun da fari dai yayin wani taron majalisar iimi ta kasa karo na 66 ranar alhamis a birnin tarayya abuja an jiwo ministan na bayyana cewa ya gaza a matsayin sa na ministan ilimi a kasar.

Wannan kamalami na ministan na zuwa ne bayan gazawa da yayi wajen warware kalubalen da dama daya kamata ya warware kasancewar sa minister mafi dadea akan harkokin ilimi a kasar.

Sai dai yayin jawabin ya zargi ma’aikatun ilimi na jihohi da kara ingiza wasu abubuwa da suka taimaka wajen gazawar ta sa matsayin ministan ilimi.

Yace kama daga kan karin yawan yaran da basa zuwa makaranta da aka samu a kasar har zuwa ga kalubalen kungiyar malaman jami’oin kasar ta ASUU da sauran da sauran matsalolin dake kara tabarbara harkokin ilimi manyan makarantu, wanda ya gaza samar da mafitar shawo kan matsalolin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp