Home Labarai Kamfanin Emirates ya soke zirga-zirga zuwa Nijeriya

Kamfanin Emirates ya soke zirga-zirga zuwa Nijeriya

Kamfanin sufurin jiragen sama na Emirates ya soke zirga-zirga zuwa Najeriya saboda kuɗaɗensa da ya ce gwamnatin ƙasar ta hana shi taɓawa.

Kamfanin na Daular Larabawa ya ƙara da cewa har yanzu bai samu kasonsa ba na dala miliyan 260 da Babban Bankin Najeriya (CBN) ya sakar wa kamfanonin ƙasar waje na kuɗin tikiti da suka sayar a Najeriyar.

A watan Satumba ne Emirates ya koma zirga-zirga a Najeriya bayan CBN ya sanar da sakin kuɗin, wanda wani ɓangare ne na fiye da dala miliyan 600 da kamfanonin jiragen ke son kwashewa zuwa ƙasashensu na asali.

“Har yanzu Emirates bai samu nasa kason ba daga cikin kuɗin da ya kamata ya kai gida,” a cewar sanarwar da ya fitar ranar Alhamis.

“Idan ba a kwashe kuɗin zuwa gida ba kuma ba tare da wani tsarin da zai tabbatar da cewa kuɗaɗen ba su ci gaba da taruwa ba…ba za mu iya ci gaba da aiki ba balle ma zirga-zirgarmu zuwa Najeriya.”

Ko da yake dai ana kallon wannan mataki na kamfanin matsayin wani bangare na rashin jituwar dake tsakanin daular larabawan da Nijeriyar duk da kamfanin bai fito karara ya bayyana hakan ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp