Home Labarai Kamfanin Emirates ya soke zirga-zirga zuwa Nijeriya

Kamfanin Emirates ya soke zirga-zirga zuwa Nijeriya

Kamfanin sufurin jiragen sama na Emirates ya soke zirga-zirga zuwa Najeriya saboda kuɗaɗensa da ya ce gwamnatin ƙasar ta hana shi taɓawa.

Kamfanin na Daular Larabawa ya ƙara da cewa har yanzu bai samu kasonsa ba na dala miliyan 260 da Babban Bankin Najeriya (CBN) ya sakar wa kamfanonin ƙasar waje na kuɗin tikiti da suka sayar a Najeriyar.

A watan Satumba ne Emirates ya koma zirga-zirga a Najeriya bayan CBN ya sanar da sakin kuɗin, wanda wani ɓangare ne na fiye da dala miliyan 600 da kamfanonin jiragen ke son kwashewa zuwa ƙasashensu na asali.

“Har yanzu Emirates bai samu nasa kason ba daga cikin kuɗin da ya kamata ya kai gida,” a cewar sanarwar da ya fitar ranar Alhamis.

“Idan ba a kwashe kuɗin zuwa gida ba kuma ba tare da wani tsarin da zai tabbatar da cewa kuɗaɗen ba su ci gaba da taruwa ba…ba za mu iya ci gaba da aiki ba balle ma zirga-zirgarmu zuwa Najeriya.”

Ko da yake dai ana kallon wannan mataki na kamfanin matsayin wani bangare na rashin jituwar dake tsakanin daular larabawan da Nijeriyar duk da kamfanin bai fito karara ya bayyana hakan ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp