Home Labarai Ganduje na Shirin Daukar Matakin Shari’a kan Jaridar Sahara Reporters

Ganduje na Shirin Daukar Matakin Shari’a kan Jaridar Sahara Reporters

Gwamnatin jihar Kano ta yi Allah-wadai da kakkausar murya da ikirarin wata kafar yada labarai ta yanar gizo ta yi na cewa, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na daya daga cikin gwamnoni uku da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arziki Ta’annati (EFCC) ta bayyana da boye kudade a gidajensu.

A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Malam Muhammad Garba ya fitar ta nuna cewa, hukumar EFCC ba ta lissafa sunayen gwamnonin da take zargi ba, amma jaridar ta bayyana sunan gwamnoni akan karya.

Ya ce rahoton da kafar ta fitar, ba shi da tushe a labaran bincike, sai dai kawai hasashe na mawallafa ko kuma wani yunkuri na bata sunan gwamnan da gangan.

Malam Garba ya yi nuni da cewa, Gwamna Ganduje bai boye Biliyoyin Nairori a gida ba don biyan ma’aikatan gwamnatinsa albashi, sabida gujewar faduwar banki.

Kwamishinan ya kara da cewa jihar Kano na daya daga cikin jihohin tarayya da ke biyan albashin ma’aikata akan lokaci, a lokacin da da jaridar ta fitar da rahoton karya, an fara ba wasu Ma’aikatan jihar albashin watan Oktoba.

Don haka ya yi kira ga jaridar da ta janye labarin tare da neman gafarar gwamnatin ba tare da bata lokaci ba, gwamnatin jihar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen daukar matakin shari’a.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp