Home Labarai Asusun tallafawa da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) zai bayar...

Asusun tallafawa da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) zai bayar da tallafin jin kai ga yara 21 da aka ceto a Katsina.

Asusun tallafawa da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) zai bayar da tallafin jin kai ga yara 21 da aka ceto a Katsina.

 

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin UNICEF Samuel Kalu ya fitar a ranar Talata.

Mista Kalu ya ce kulawar zata taimaka wa yaran wajen magance matsalar da kuma sake shiga cikin al’umma.

Idan dai za’a iya tuna anyi garkuwa da yaran ne masu shekaru 16 zuwa 21 a ranar 30 ga watan Oktoba a wata gona da ke Mairuwa a karamar hukumar Faskari ta Katsina.

Wadanda abin ya shafa sun hadar da ‘yan mata 17 da maza hudu, wadanda aka sami nasarar kubutar da su bayan sun kwashe kwanaki shida.

“UNICEF na maraba da labarin sakin yara 21 da aka sace a wata gona da ke karamar hukumar Faskari a jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya,” in ji hukumar ta UN.

“Muna yabawa hukuma kan matakin da ta dauka na sako yaran da aka yi garkuwa da su a ranar Asabar da ta gabata.

Sakin dukkan yaran 21 da aka sace, labari ne mai dadi a gare mu duka iyaye, masu kulawa, shugabannin al’umma, da kowa da kowa.”

Sanarwar ta kara da cewa, tun da farko bai kamata a yi garkuwa da wadannan yaran ba, domin babu wanda ya kamata a yi garkuwa da su, musamman kananan yara, ko kuma tashe-tashen hankula.

UNICEF ta kuma bayyana cewa, za ta tallafa wa ma’aikatar harkokin mata da ci gaban al’umma ta Jihar Katsina don tallafa wa yaran da aka kubutar da su “don taimaka su murmure daga halin da suke ciki da kuma komawa cikin al’umma.”

NAN

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp