Home DUNIYA Rikicin Kibilanci na ci gaba da Tsananta a Jamhuriyar Demokradiyar Congo

Rikicin Kibilanci na ci gaba da Tsananta a Jamhuriyar Demokradiyar Congo

Ana cigaba da bincike kan rikicin daya haddasa mutuwar akalla mutane 20 cikin makon nan a rikicin kabilancin da ke ci gaba da tsananta tsakanin kabilar Yaka da Teke na lardin Mai-Ndombe a Mahukuntan Jamhuriyar Demokradiyar Congo.

Tsawon watanni ana fama da rikicin kabilancin a yankin Mai-Ndombe inda alkaluman gwamnatin kasar ke cewa daga faro fadan a watan Yunin da ya gabata zuwa yanzu an kashe fararen hulan da yawansu yah aura 180 ciki har da wasu 16 a makon jiya kari kan mutane 20 da aka kashe a cikin makon nan.

Majiyoyi daga yankin sun ce rikicin ya faro bayan takaddama game da biyan haraji lamarin da zuwa yanzu ya tilasta dubunnan mutane daga kabilun biyu na Yaka da Teke tserewa daga yankunansu don tsira da rayukansu.

Duk da cewa kamfanin dillancin labaran Faransa ya gaza tattara hakikanin alkaluman mutanen da rikicin ya daidaita da kuma wadanda suka mutu, amma Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa matukar ba a dauka matakan da suka kamata ba, rikicin ka iya juyewa zuwa mafi muni.

Rahotanni sun ce a litinin din da ta gabata ne, wasu maharan kabilar Yaka rike manyan bindigu suka farwa kauyen Teke lamarin da ya sanya al’ummar garin kare kansu ta hanyar daukar makamai inda nan take akayi asarar rayukan mutane akalla 20.

Wani ganau a yankin na Teke, Nkete Mboma Butu y ace adadin mutanen da suka mutu ka iya zarta alkaluman da mahukuntan kasar suka bayyana la’akari da yadda aka samu asarar rayuka daga dukkanin bangarorin biyu.

Da ya ke bayar da bahasi kan rikicin na makon nan yayin jawabinsa gaban wakilan gwamnati a Kinshasa mataimakin shugaban yankin Moise Makami Muzik ya ce alkaluman mutanen da suka mutu a rikicin ya haura 35.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp