Home DUNIYA Rikicin Kibilanci na ci gaba da Tsananta a Jamhuriyar Demokradiyar Congo

Rikicin Kibilanci na ci gaba da Tsananta a Jamhuriyar Demokradiyar Congo

Ana cigaba da bincike kan rikicin daya haddasa mutuwar akalla mutane 20 cikin makon nan a rikicin kabilancin da ke ci gaba da tsananta tsakanin kabilar Yaka da Teke na lardin Mai-Ndombe a Mahukuntan Jamhuriyar Demokradiyar Congo.

Tsawon watanni ana fama da rikicin kabilancin a yankin Mai-Ndombe inda alkaluman gwamnatin kasar ke cewa daga faro fadan a watan Yunin da ya gabata zuwa yanzu an kashe fararen hulan da yawansu yah aura 180 ciki har da wasu 16 a makon jiya kari kan mutane 20 da aka kashe a cikin makon nan.

Majiyoyi daga yankin sun ce rikicin ya faro bayan takaddama game da biyan haraji lamarin da zuwa yanzu ya tilasta dubunnan mutane daga kabilun biyu na Yaka da Teke tserewa daga yankunansu don tsira da rayukansu.

Duk da cewa kamfanin dillancin labaran Faransa ya gaza tattara hakikanin alkaluman mutanen da rikicin ya daidaita da kuma wadanda suka mutu, amma Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa matukar ba a dauka matakan da suka kamata ba, rikicin ka iya juyewa zuwa mafi muni.

Rahotanni sun ce a litinin din da ta gabata ne, wasu maharan kabilar Yaka rike manyan bindigu suka farwa kauyen Teke lamarin da ya sanya al’ummar garin kare kansu ta hanyar daukar makamai inda nan take akayi asarar rayukan mutane akalla 20.

Wani ganau a yankin na Teke, Nkete Mboma Butu y ace adadin mutanen da suka mutu ka iya zarta alkaluman da mahukuntan kasar suka bayyana la’akari da yadda aka samu asarar rayuka daga dukkanin bangarorin biyu.

Da ya ke bayar da bahasi kan rikicin na makon nan yayin jawabinsa gaban wakilan gwamnati a Kinshasa mataimakin shugaban yankin Moise Makami Muzik ya ce alkaluman mutanen da suka mutu a rikicin ya haura 35.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp