Home DUNIYA Rikicin Kibilanci na ci gaba da Tsananta a Jamhuriyar Demokradiyar Congo

Rikicin Kibilanci na ci gaba da Tsananta a Jamhuriyar Demokradiyar Congo

Ana cigaba da bincike kan rikicin daya haddasa mutuwar akalla mutane 20 cikin makon nan a rikicin kabilancin da ke ci gaba da tsananta tsakanin kabilar Yaka da Teke na lardin Mai-Ndombe a Mahukuntan Jamhuriyar Demokradiyar Congo.

Tsawon watanni ana fama da rikicin kabilancin a yankin Mai-Ndombe inda alkaluman gwamnatin kasar ke cewa daga faro fadan a watan Yunin da ya gabata zuwa yanzu an kashe fararen hulan da yawansu yah aura 180 ciki har da wasu 16 a makon jiya kari kan mutane 20 da aka kashe a cikin makon nan.

Majiyoyi daga yankin sun ce rikicin ya faro bayan takaddama game da biyan haraji lamarin da zuwa yanzu ya tilasta dubunnan mutane daga kabilun biyu na Yaka da Teke tserewa daga yankunansu don tsira da rayukansu.

Duk da cewa kamfanin dillancin labaran Faransa ya gaza tattara hakikanin alkaluman mutanen da rikicin ya daidaita da kuma wadanda suka mutu, amma Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa matukar ba a dauka matakan da suka kamata ba, rikicin ka iya juyewa zuwa mafi muni.

Rahotanni sun ce a litinin din da ta gabata ne, wasu maharan kabilar Yaka rike manyan bindigu suka farwa kauyen Teke lamarin da ya sanya al’ummar garin kare kansu ta hanyar daukar makamai inda nan take akayi asarar rayukan mutane akalla 20.

Wani ganau a yankin na Teke, Nkete Mboma Butu y ace adadin mutanen da suka mutu ka iya zarta alkaluman da mahukuntan kasar suka bayyana la’akari da yadda aka samu asarar rayuka daga dukkanin bangarorin biyu.

Da ya ke bayar da bahasi kan rikicin na makon nan yayin jawabinsa gaban wakilan gwamnati a Kinshasa mataimakin shugaban yankin Moise Makami Muzik ya ce alkaluman mutanen da suka mutu a rikicin ya haura 35.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp