Home Labarai Asusun tallafawa da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) zai bayar...

Asusun tallafawa da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) zai bayar da tallafin jin kai ga yara 21 da aka ceto a Katsina.

Asusun tallafawa da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) zai bayar da tallafin jin kai ga yara 21 da aka ceto a Katsina.

 

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin UNICEF Samuel Kalu ya fitar a ranar Talata.

Mista Kalu ya ce kulawar zata taimaka wa yaran wajen magance matsalar da kuma sake shiga cikin al’umma.

Idan dai za’a iya tuna anyi garkuwa da yaran ne masu shekaru 16 zuwa 21 a ranar 30 ga watan Oktoba a wata gona da ke Mairuwa a karamar hukumar Faskari ta Katsina.

Wadanda abin ya shafa sun hadar da ‘yan mata 17 da maza hudu, wadanda aka sami nasarar kubutar da su bayan sun kwashe kwanaki shida.

“UNICEF na maraba da labarin sakin yara 21 da aka sace a wata gona da ke karamar hukumar Faskari a jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya,” in ji hukumar ta UN.

“Muna yabawa hukuma kan matakin da ta dauka na sako yaran da aka yi garkuwa da su a ranar Asabar da ta gabata.

Sakin dukkan yaran 21 da aka sace, labari ne mai dadi a gare mu duka iyaye, masu kulawa, shugabannin al’umma, da kowa da kowa.”

Sanarwar ta kara da cewa, tun da farko bai kamata a yi garkuwa da wadannan yaran ba, domin babu wanda ya kamata a yi garkuwa da su, musamman kananan yara, ko kuma tashe-tashen hankula.

UNICEF ta kuma bayyana cewa, za ta tallafa wa ma’aikatar harkokin mata da ci gaban al’umma ta Jihar Katsina don tallafa wa yaran da aka kubutar da su “don taimaka su murmure daga halin da suke ciki da kuma komawa cikin al’umma.”

NAN

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp