Home Labarai Asusun tallafawa da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) zai bayar...

Asusun tallafawa da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) zai bayar da tallafin jin kai ga yara 21 da aka ceto a Katsina.

Asusun tallafawa da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) zai bayar da tallafin jin kai ga yara 21 da aka ceto a Katsina.

 

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin UNICEF Samuel Kalu ya fitar a ranar Talata.

Mista Kalu ya ce kulawar zata taimaka wa yaran wajen magance matsalar da kuma sake shiga cikin al’umma.

Idan dai za’a iya tuna anyi garkuwa da yaran ne masu shekaru 16 zuwa 21 a ranar 30 ga watan Oktoba a wata gona da ke Mairuwa a karamar hukumar Faskari ta Katsina.

Wadanda abin ya shafa sun hadar da ‘yan mata 17 da maza hudu, wadanda aka sami nasarar kubutar da su bayan sun kwashe kwanaki shida.

“UNICEF na maraba da labarin sakin yara 21 da aka sace a wata gona da ke karamar hukumar Faskari a jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya,” in ji hukumar ta UN.

“Muna yabawa hukuma kan matakin da ta dauka na sako yaran da aka yi garkuwa da su a ranar Asabar da ta gabata.

Sakin dukkan yaran 21 da aka sace, labari ne mai dadi a gare mu duka iyaye, masu kulawa, shugabannin al’umma, da kowa da kowa.”

Sanarwar ta kara da cewa, tun da farko bai kamata a yi garkuwa da wadannan yaran ba, domin babu wanda ya kamata a yi garkuwa da su, musamman kananan yara, ko kuma tashe-tashen hankula.

UNICEF ta kuma bayyana cewa, za ta tallafa wa ma’aikatar harkokin mata da ci gaban al’umma ta Jihar Katsina don tallafa wa yaran da aka kubutar da su “don taimaka su murmure daga halin da suke ciki da kuma komawa cikin al’umma.”

NAN

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp