Home Labarai ASUU Tace Bazata Sake Shiga Yajin Aiki ba

ASUU Tace Bazata Sake Shiga Yajin Aiki ba

Kungiyar Malaman jami’o’I Nijeriya (ASUU) ta kawo karshen taronta na kwamitin zartarwa na kasa (NEC) inda ta yanke matsayar ba zata sake shiga wani yajin aiki ba.

Sai dai kungiyar ta yi Allah-wadai da yunkurin gwamnatin tarayya na mayar da malaman jami’o’i kamar ma’aikatan wucin gadi ta hanyar biyansu Rabin albashin su.

A wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a ranar Talata bayan kammala taron NEC, shugaban ASUU na kasa, Farfesa Emmanuel Osodeke, ya bayyana cewa malaman jami’o’in cikakakkun ma’aikata ne ba na wucin gadi ba.

Ya ce kungiyar ta dakatar da yajin aikin na watanni takwas a ranar 14 ga Oktoba, 2022 bisa bin umarnin kotun ma’aikata ta kasa da kuma la’akari da kokarin tsoma bakin ‘yan Najeriya masu kishin kasa, ciki har da Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Femi Gbajabiamila.

Osodeke ya kara da cewa matakin da kungiyar ta dauka alamu ne da suka nuna tsantsar biyayyar ta ga bangaren shari’a, da sauran cibiyoyi da ma’aikatun gwamnati a kodayaushe da suke kira ga kungiyar data sanya kishin kasa fiye da bukatun kansu.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp