Home DUNIYA Burtaniya ta Janye Gargadin Yiwuwar Kai Hari Birni Abuja

Burtaniya ta Janye Gargadin Yiwuwar Kai Hari Birni Abuja

Birtaniya ta janye gargadin da ta yi ga al’ummarta game da yiwuwar hare-haren ta’addanci a babban birnin Najeriya Abuja, inda ta ce a yanzu al’amura sun fara daidaita a birnin saboda daukar matakan kawar da waccan barazana da mahukuntan kasar suka yi.

Makwanni biyu bayan Ofishin jakadancin Birtaniyar ya bi sahun takwarorinsa na Amurka da Italiya wajen gargadin al’ummominsu da ke rayuwa a Najeriya kan su kauracewa ziyartar wasu sassa na kasar musamman birnin Tarayya Abuja game da yiwuwar hare-haren ta’addanci, Ofishin ya yi sake Magana da yayi tun da fari inda ya bayyana cewa yanzu barazanar ta kau a Abuja, sai dai har yanzu babu cikakken tsaro.

Wata sanarwar ofishin kula harkokin ci gaban kasashen renon Ingila na FCDO da ya wallafa a shafinta jiya litinin, ta ce ta janye batun hana al’ummominta bulaguro zuwa Abuja duk da cewa har yanzu akwai barazanar tsaron, sai dai ta ce har yanzu hanin ya na nan kan sauran sassan kasar musamman jihohin arewaci.

Ofishin na FCDO ya sabunta gargadi kan ziyarta jihohin Borno da Yobe da Adamawa da Gombe da Kaduna da kuma Katsina baya ga Zamfara da Delta, da Bayelsa da Rivers da Akwa Ibom da kuma Cross River wadanda Ofishin ya ce suna fama da barazanar hare-haren ta’addanci .

Sanarwar ta ce bata sauya zani ba, game da barazanar hare-haren ta’addancin da ake fuskanta a jihohin Bauchi da Kano da Jigawa da Neja da Sokoto da Kogi State baya ga wani yanki na jihar Kebbi mai tazarar kilomita 20 da jihar Neja kana jihar Abia sai kuma wasu sassa na jihohin Delta da Bayelsa da Rivers da Pulato da Taraba.

Ofishin ya shawarci matafiya da su rika duba sanarwar hukumomi game da yanayin tsaron yankin kafin kai ziyara yayinda yace mafi dacewa shi ne al’ummomin na Birtaniya su kaucewa zuwa jihohin haka zalika su yi taka-tsan-tsan da ratsawa wata kasa a kokarinsu na komawa gida.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp