Home DUNIYA Burtaniya ta Janye Gargadin Yiwuwar Kai Hari Birni Abuja

Burtaniya ta Janye Gargadin Yiwuwar Kai Hari Birni Abuja

Birtaniya ta janye gargadin da ta yi ga al’ummarta game da yiwuwar hare-haren ta’addanci a babban birnin Najeriya Abuja, inda ta ce a yanzu al’amura sun fara daidaita a birnin saboda daukar matakan kawar da waccan barazana da mahukuntan kasar suka yi.

Makwanni biyu bayan Ofishin jakadancin Birtaniyar ya bi sahun takwarorinsa na Amurka da Italiya wajen gargadin al’ummominsu da ke rayuwa a Najeriya kan su kauracewa ziyartar wasu sassa na kasar musamman birnin Tarayya Abuja game da yiwuwar hare-haren ta’addanci, Ofishin ya yi sake Magana da yayi tun da fari inda ya bayyana cewa yanzu barazanar ta kau a Abuja, sai dai har yanzu babu cikakken tsaro.

Wata sanarwar ofishin kula harkokin ci gaban kasashen renon Ingila na FCDO da ya wallafa a shafinta jiya litinin, ta ce ta janye batun hana al’ummominta bulaguro zuwa Abuja duk da cewa har yanzu akwai barazanar tsaron, sai dai ta ce har yanzu hanin ya na nan kan sauran sassan kasar musamman jihohin arewaci.

Ofishin na FCDO ya sabunta gargadi kan ziyarta jihohin Borno da Yobe da Adamawa da Gombe da Kaduna da kuma Katsina baya ga Zamfara da Delta, da Bayelsa da Rivers da Akwa Ibom da kuma Cross River wadanda Ofishin ya ce suna fama da barazanar hare-haren ta’addanci .

Sanarwar ta ce bata sauya zani ba, game da barazanar hare-haren ta’addancin da ake fuskanta a jihohin Bauchi da Kano da Jigawa da Neja da Sokoto da Kogi State baya ga wani yanki na jihar Kebbi mai tazarar kilomita 20 da jihar Neja kana jihar Abia sai kuma wasu sassa na jihohin Delta da Bayelsa da Rivers da Pulato da Taraba.

Ofishin ya shawarci matafiya da su rika duba sanarwar hukumomi game da yanayin tsaron yankin kafin kai ziyara yayinda yace mafi dacewa shi ne al’ummomin na Birtaniya su kaucewa zuwa jihohin haka zalika su yi taka-tsan-tsan da ratsawa wata kasa a kokarinsu na komawa gida.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp