Home DUNIYA Iran ta Kera Sabon Samfurin Makami Mai Linzami

Iran ta Kera Sabon Samfurin Makami Mai Linzami

Iran ta ce ta kera wani makami mai linzami mai matsanancin gudu da ka iya ratsa duk wani tsarin tsaro da aka shimfida, kamar yadda babban kwamandan rundunar juyin juye hali ta kasar Amirali Hajizadeh ya bayyana a yau Alhamis.

Wannan shu’umin makami mai linzami, kamar sauran makamai masu cin dogon zango, yana da gudun da ya ninka sauti har sau 5.

Hajizadeh ya ce an yi wannan makami ne don iya waske duk wani tsari na tsaron makami mai linzami, inda ya kara da cewa zai dau gwamman shekaru kafin a samar da wani tsarin tsaro da zai dakile shi.

Wannan sanarwar na zuwa ne kwanaki bayan da iran ta amsa zargin cewa ita ta bai wa Rasha jirage marasa matuka, amma ta musanta cewa ta bada jiragen ne bayan mamayar Ukraine.

Akasin makami mai cin dogon zango, wannan makami mai linzami yana tafiya ne a kasa kasa da sararin samaniya, lamarin da ya sa yake iya kai wa ga inda aka harba shi da wuri.

Gwajin irin wannan makami da Korea ta Arewa ta yi a shekarar da ta gabata ya haddasa damuwa a kan rige rigen samun makamancin makamin.

A yayin da kasashe kamar su Amurka suka samar da na’urori da ke bada kariya ga makami mai linzami da ke cin dogon zango, taka wa wannan shu’umin makami birki na da matukar wahala.

tushe RFI

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp