Home DUNIYA Iran ta Kera Sabon Samfurin Makami Mai Linzami

Iran ta Kera Sabon Samfurin Makami Mai Linzami

Iran ta ce ta kera wani makami mai linzami mai matsanancin gudu da ka iya ratsa duk wani tsarin tsaro da aka shimfida, kamar yadda babban kwamandan rundunar juyin juye hali ta kasar Amirali Hajizadeh ya bayyana a yau Alhamis.

Wannan shu’umin makami mai linzami, kamar sauran makamai masu cin dogon zango, yana da gudun da ya ninka sauti har sau 5.

Hajizadeh ya ce an yi wannan makami ne don iya waske duk wani tsari na tsaron makami mai linzami, inda ya kara da cewa zai dau gwamman shekaru kafin a samar da wani tsarin tsaro da zai dakile shi.

Wannan sanarwar na zuwa ne kwanaki bayan da iran ta amsa zargin cewa ita ta bai wa Rasha jirage marasa matuka, amma ta musanta cewa ta bada jiragen ne bayan mamayar Ukraine.

Akasin makami mai cin dogon zango, wannan makami mai linzami yana tafiya ne a kasa kasa da sararin samaniya, lamarin da ya sa yake iya kai wa ga inda aka harba shi da wuri.

Gwajin irin wannan makami da Korea ta Arewa ta yi a shekarar da ta gabata ya haddasa damuwa a kan rige rigen samun makamancin makamin.

A yayin da kasashe kamar su Amurka suka samar da na’urori da ke bada kariya ga makami mai linzami da ke cin dogon zango, taka wa wannan shu’umin makami birki na da matukar wahala.

tushe RFI

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp