Home Labarai Kwamishin ‘Yan Sandan jihar Zamfara na ziyarar tabbatar da Zaman lafiya a...

Kwamishin ‘Yan Sandan jihar Zamfara na ziyarar tabbatar da Zaman lafiya a Jihar

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara, CP Kolo Yusuf PSC, ya ziyarci sansanin wucin gadi na horas da masu hidimar kasa dake makarantar sakandiren ta kimiyya dake Gusau
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da kwanan watan 11 ga watan Nuwamba 2022 da kakakin rundunar yan sandan jihar SP Muhammad Shehu ANIPR ya aikowa da PRNigeria.

Inda sanarwa tace ziyarar na wani bangare na tabbatar da zaman lafiya a jihar dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Kwamishinan ya kai ziyarar ne domin ingantawa gami da karfafa tsare-tsaren tsaron a sansanin da nufin tabbatar da tsare dukkan masu hidimar kasa dake jihar baki daya.
A yayin jawabin sa ga masu hidimar kasar kwamishinan ‘yan sanda ya basu tabbatacin cewa ‘yan sanda zasu jajirce wajen kare rayukan su a sansanin da kuma wurare.

Daga bisani ya bukace su dasu kasance masu lura gami da kai rahoton ga ‘yan sanda da sauran hukumin tsaro kan dukkan abinda ya shige musu duhu domin daukar matakan gaggawa.

ko dai a cikin wannan mako an gano kwamishinan na wata ziyarar zuwa Jami’ar gwamnatin tarayya dake Gusau da kwalejin Ilimi da kere-kere ta tarayya, gami da Makarantar sakandire da “yan sanda dake jihar.

Jihar Zamfara dai na guda cikin jihohin dake Arewacin Nijeriya dake fama da matsalolin rashin tsaro sakamakon ‘yan bindiga masu satar mutane domin karbar kudin fansa da wasu matsaloli da ke da alaka da rashin tsaro a jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp