Kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara, CP Kolo Yusuf PSC, ya ziyarci sansanin wucin gadi na horas da masu hidimar kasa dake makarantar sakandiren ta kimiyya dake Gusau
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da kwanan watan 11 ga watan Nuwamba 2022 da kakakin rundunar yan sandan jihar SP Muhammad Shehu ANIPR ya aikowa da PRNigeria.
Inda sanarwa tace ziyarar na wani bangare na tabbatar da zaman lafiya a jihar dake arewa maso yammacin Nijeriya.
Read Also:
Kwamishinan ya kai ziyarar ne domin ingantawa gami da karfafa tsare-tsaren tsaron a sansanin da nufin tabbatar da tsare dukkan masu hidimar kasa dake jihar baki daya.
A yayin jawabin sa ga masu hidimar kasar kwamishinan ‘yan sanda ya basu tabbatacin cewa ‘yan sanda zasu jajirce wajen kare rayukan su a sansanin da kuma wurare.
Daga bisani ya bukace su dasu kasance masu lura gami da kai rahoton ga ‘yan sanda da sauran hukumin tsaro kan dukkan abinda ya shige musu duhu domin daukar matakan gaggawa.
ko dai a cikin wannan mako an gano kwamishinan na wata ziyarar zuwa Jami’ar gwamnatin tarayya dake Gusau da kwalejin Ilimi da kere-kere ta tarayya, gami da Makarantar sakandire da “yan sanda dake jihar.
Jihar Zamfara dai na guda cikin jihohin dake Arewacin Nijeriya dake fama da matsalolin rashin tsaro sakamakon ‘yan bindiga masu satar mutane domin karbar kudin fansa da wasu matsaloli da ke da alaka da rashin tsaro a jihar.











