Home Labarai Kwamishin ‘Yan Sandan jihar Zamfara na ziyarar tabbatar da Zaman lafiya a...

Kwamishin ‘Yan Sandan jihar Zamfara na ziyarar tabbatar da Zaman lafiya a Jihar

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara, CP Kolo Yusuf PSC, ya ziyarci sansanin wucin gadi na horas da masu hidimar kasa dake makarantar sakandiren ta kimiyya dake Gusau
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da kwanan watan 11 ga watan Nuwamba 2022 da kakakin rundunar yan sandan jihar SP Muhammad Shehu ANIPR ya aikowa da PRNigeria.

Inda sanarwa tace ziyarar na wani bangare na tabbatar da zaman lafiya a jihar dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Kwamishinan ya kai ziyarar ne domin ingantawa gami da karfafa tsare-tsaren tsaron a sansanin da nufin tabbatar da tsare dukkan masu hidimar kasa dake jihar baki daya.
A yayin jawabin sa ga masu hidimar kasar kwamishinan ‘yan sanda ya basu tabbatacin cewa ‘yan sanda zasu jajirce wajen kare rayukan su a sansanin da kuma wurare.

Daga bisani ya bukace su dasu kasance masu lura gami da kai rahoton ga ‘yan sanda da sauran hukumin tsaro kan dukkan abinda ya shige musu duhu domin daukar matakan gaggawa.

ko dai a cikin wannan mako an gano kwamishinan na wata ziyarar zuwa Jami’ar gwamnatin tarayya dake Gusau da kwalejin Ilimi da kere-kere ta tarayya, gami da Makarantar sakandire da “yan sanda dake jihar.

Jihar Zamfara dai na guda cikin jihohin dake Arewacin Nijeriya dake fama da matsalolin rashin tsaro sakamakon ‘yan bindiga masu satar mutane domin karbar kudin fansa da wasu matsaloli da ke da alaka da rashin tsaro a jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp