Home Labarai Kwamishin ‘Yan Sandan jihar Zamfara na ziyarar tabbatar da Zaman lafiya a...

Kwamishin ‘Yan Sandan jihar Zamfara na ziyarar tabbatar da Zaman lafiya a Jihar

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara, CP Kolo Yusuf PSC, ya ziyarci sansanin wucin gadi na horas da masu hidimar kasa dake makarantar sakandiren ta kimiyya dake Gusau
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da kwanan watan 11 ga watan Nuwamba 2022 da kakakin rundunar yan sandan jihar SP Muhammad Shehu ANIPR ya aikowa da PRNigeria.

Inda sanarwa tace ziyarar na wani bangare na tabbatar da zaman lafiya a jihar dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Kwamishinan ya kai ziyarar ne domin ingantawa gami da karfafa tsare-tsaren tsaron a sansanin da nufin tabbatar da tsare dukkan masu hidimar kasa dake jihar baki daya.
A yayin jawabin sa ga masu hidimar kasar kwamishinan ‘yan sanda ya basu tabbatacin cewa ‘yan sanda zasu jajirce wajen kare rayukan su a sansanin da kuma wurare.

Daga bisani ya bukace su dasu kasance masu lura gami da kai rahoton ga ‘yan sanda da sauran hukumin tsaro kan dukkan abinda ya shige musu duhu domin daukar matakan gaggawa.

ko dai a cikin wannan mako an gano kwamishinan na wata ziyarar zuwa Jami’ar gwamnatin tarayya dake Gusau da kwalejin Ilimi da kere-kere ta tarayya, gami da Makarantar sakandire da “yan sanda dake jihar.

Jihar Zamfara dai na guda cikin jihohin dake Arewacin Nijeriya dake fama da matsalolin rashin tsaro sakamakon ‘yan bindiga masu satar mutane domin karbar kudin fansa da wasu matsaloli da ke da alaka da rashin tsaro a jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp