‘Yan Bindiga Sun Sace Hakimi a Jihar Zamfara

Rahotanni daga jihar Zamfara dake arewa maso yammacin Najeriya na bayyana cewa ‘Yan bindiga sun yi awon gaba da hakimin gundumar Kwangami a karamar hukumar Zurmi ta jihar tare da wasu mutane 6.

Majiyoyi daga yankin sun ce ‘yan bindigar sun shiga garin ne da manyan makamai a ranar Litinin, inda suka jefa al’ummar kauyen cikin rudani, kuma suka dauke basaraken, Alhaji Muhammad Galadima.

Sun kara da cewa ‘yan ta’addan sun bi wadannan mutane har gidajensu ne suka dauke su.

A waje daya kuma, ‘yan bindiga ssun sako mutane 6  da suka sace a kauyen Kazauda na karamar hukumar Gusau a jihar Zamfara bayan da aka biya Naira miliyan 4 a matsayin kudin fansa.

Kawo yanzu dai rundunar ‘yan sandan jihar ba tace ba komai kan wannan batu.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 40 minutes 34 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 21 minutes 59 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com