Home SIYASA Gwamnatin Jihar Katsina Ta Ayyana Dokar Hana Amfani da ‘Yan Daba a...

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Ayyana Dokar Hana Amfani da ‘Yan Daba a Zaben 2023

Gwamnan jihar Katsina ya ayyana dokar hana amfani da ‘yan daba a zaben 2023 mai zuwa nan da badi.

Ya bayyana hakan ne ta bakin mai ba shi shawari kan harkokin tsaro, ya kuma ba ‘yan siyasa shawari mai kyau.

Gamayyar kungiyar farar hula ta yabawa gwamnan, ta kuma bayyana kwarin gwiwar samun zabe na gari a Katsina.

Jihar Katsina – A kokarin tabbatar da zaben 2023 cikin aminci, gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari ya sanya hannun kan dokar hana damawa da ‘yan daba a gangamin zabe a fadin jiharsa, AIT ta ruwaito.

Gwamnan ya bayyana wannan ne ta bakin mai ba shi shawari kan harkokin tsaro, Ibrahim Katsina, kuma ya ce hakan zai taimaka wajen tabbatar da zaban shugabannin da suka dace a zaben da za yi.

Ya kuma bayyana cewa, tunda wannan ne zaben karshe da za a yi a mulkin Masari, yana da kyau a yi shi cikin aminci domin kafa tarihi na gari a jihar.

Hakazalika, ya ce gwamna Masari dattijon kasa ne, kuma zai tabbatar da zaman lafiya a jihar, musamman a kokarinsa na dawo da martabar jihar a matsayin kasa mai tarbar baki.

Ku dauki ‘ya’yan talakawa kamar naku, Masari ga ‘yan siyasa

Daga karshe ya shawarci ‘yan siyasa da suke yiwa ‘yan daba kallon ‘ya’yansu kuma ya kamata su ba su wadataccen ilimi a madadin bata rayuwarsu ta hanyar mai dasu tsageru.

Shugaban Gamayyar Kungiyoyin Farar Hula ta CCSO, Abdulrahman Abdullahi ya yaba da kokarin Masari na damawa da ‘yan daba, tare da bayyana cewa hakan zai tabbatar da zabe na gari a Katsina.

Daga nan ne ya ce, idan gwamnati ta tabbatar da cikakken amfani da dokar, zai zama mafi alherin abin da gwamnan ya assasa.

Ko da a baya an taba jiyo yadda gwamnan ya yi irin wannan hani a watan Fabrairun 2022.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp