Home SIYASA Gwamnan Jihar Benuwai, Samuel Ortom Yace Bazai Zabi Bafullatani ba.

Gwamnan Jihar Benuwai, Samuel Ortom Yace Bazai Zabi Bafullatani ba.

Gwamnan jihar Benuwai, Samuel Ortom, yace ba zai mara wa ɗan takarar PDP, Atiku Abubakar baya ba a zaben shekarar 2023.

Gwamnan, wanda ya fito daga arewacin Najeriya yace ya gwammaci ya mutu da ya goyi bayan Bafullatani ya zama shugaban ƙasa.

Ortom na ɗaya daga cikin tawagar gwamnoni 5 da suka ware kansu a PDP kuma suka nemi Ayu ya yi murabus.

An ruwaito Gwamnna Ortom na faɗa wa Atiku cewa can ta matse masa, amma ba zai mara masa baya ba yayin da Fulani ke kashe mutanensa a Benuwai.

Ortom ya yi wannan furucin ne ranar Lahadi da daddare yayin da ya karɓi bakuncin gwamnonin 5 G-5 da suka haɗa da, Nyesom Wike na Ribas, Okezie Ikpeazu na Abiya; Seyi Makinde na Oyo da Ifeanyi Ugwuanyi na Enugu.

Gwamnan ya koka da kisan da aka yi wa mutane 18 a ƙaramar hukumar da ya fito a makon da ya gabata,

“Can ta matse wa Atiku da duk masu goyon bayansa, ku je ku gaya masa shin yana son na zama bawan Fulani ne? Gara na mutu, duk mai ƙaunar Atiku maƙiyin jihar Benuwai ne.” “Ana ta kashe mutane na amma ku ce in yi shiru”.

Wa’adin mulkina zai kare a watan Mayu, daga nan zaku iya mun duk abinda kuka ga dama idan kuna tunanin kuna da mulki, na riga na rubuta wasiyyata.”

“Lokacin da na baiwa matata wasiyyata, shafe dare ta yi tana kuka. Idan na mutu a 62 da yawan sa’annina sun riga ni tafiya. Idan yanzun na mutu na cimma nasara amma kowa ya sani na mutu ne a kokarin kare rayuwar mutane na.”

Ba zan taba goyon bayan Bafillatani ya zama shugaban kasa ba – Ortom Bugu da ƙari, Gwamna Ortom.yace ba zai taɓa tallafa wa Fulani da ɗare kujerar shugaban ƙasa ba a Najeriya.”

“Ba zan taɓa goyon bayan Bafillatani ya zama shugaban ƙasa ba, idan akwai wani mutum da ke bukatar aiki da ni da tabbatar da tsare rayukan mutanena, an shirya aiki da shi.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp