Home SIYASA Gwamnan Jihar Benuwai, Samuel Ortom Yace Bazai Zabi Bafullatani ba.

Gwamnan Jihar Benuwai, Samuel Ortom Yace Bazai Zabi Bafullatani ba.

Gwamnan jihar Benuwai, Samuel Ortom, yace ba zai mara wa ɗan takarar PDP, Atiku Abubakar baya ba a zaben shekarar 2023.

Gwamnan, wanda ya fito daga arewacin Najeriya yace ya gwammaci ya mutu da ya goyi bayan Bafullatani ya zama shugaban ƙasa.

Ortom na ɗaya daga cikin tawagar gwamnoni 5 da suka ware kansu a PDP kuma suka nemi Ayu ya yi murabus.

An ruwaito Gwamnna Ortom na faɗa wa Atiku cewa can ta matse masa, amma ba zai mara masa baya ba yayin da Fulani ke kashe mutanensa a Benuwai.

Ortom ya yi wannan furucin ne ranar Lahadi da daddare yayin da ya karɓi bakuncin gwamnonin 5 G-5 da suka haɗa da, Nyesom Wike na Ribas, Okezie Ikpeazu na Abiya; Seyi Makinde na Oyo da Ifeanyi Ugwuanyi na Enugu.

Gwamnan ya koka da kisan da aka yi wa mutane 18 a ƙaramar hukumar da ya fito a makon da ya gabata,

“Can ta matse wa Atiku da duk masu goyon bayansa, ku je ku gaya masa shin yana son na zama bawan Fulani ne? Gara na mutu, duk mai ƙaunar Atiku maƙiyin jihar Benuwai ne.” “Ana ta kashe mutane na amma ku ce in yi shiru”.

Wa’adin mulkina zai kare a watan Mayu, daga nan zaku iya mun duk abinda kuka ga dama idan kuna tunanin kuna da mulki, na riga na rubuta wasiyyata.”

“Lokacin da na baiwa matata wasiyyata, shafe dare ta yi tana kuka. Idan na mutu a 62 da yawan sa’annina sun riga ni tafiya. Idan yanzun na mutu na cimma nasara amma kowa ya sani na mutu ne a kokarin kare rayuwar mutane na.”

Ba zan taba goyon bayan Bafillatani ya zama shugaban kasa ba – Ortom Bugu da ƙari, Gwamna Ortom.yace ba zai taɓa tallafa wa Fulani da ɗare kujerar shugaban ƙasa ba a Najeriya.”

“Ba zan taɓa goyon bayan Bafillatani ya zama shugaban ƙasa ba, idan akwai wani mutum da ke bukatar aiki da ni da tabbatar da tsare rayukan mutanena, an shirya aiki da shi.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp