Ghana ta Gargadi ‘yan kasarta kan zuwa Nijeriya

Gwamnatin Ghana ta gargadi ‘yan kasarta kan balaguro zuwa babban birnin tarayyar Najeriya Abuja saboda matsalar tsaro.

Wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar ranar Laraba ta ce gargadin ya biyo bayan mawuyacin hali da ake ciki a babban birnin kasar da kuma umarnin da hukumomi Najeriya suka bayar na a rufe otal-otal da ke gidajen kwana.

Sanarwar ta ta bukaci ‘yan kasar Ghana da dole sai sun shiga birnin Abuja da su tabbaatar sun dauki matakin kariya da taka tsan-tsan, inda ma’aikatar za ta ci gaba da sanya ido kan yadda al’umara ke ganuna tare da bayar da bayanai ga jama’a idan lamarin ya daidaita.”

Ana yawan tafiye-tafiye tsakanin Ghana da Najeriya, manyan kasashe biyu mafi karfin tattalin arziki a yammacin Afirka.

Hakan na zuwa ne makonni bayan Amurka da wasu ofisoshin jakadancin kasashen waje sun yi gargadi game da tafiye-tafiye zuwa babban birnin Najeriya saboda barazanar ta’addanci.

Sai dai gwamnatin Najeriya ta roki ‘yan kasar da su kwantar da hankulansu tana mai tabbatar musu da cewa jami’an tsaro na kokarin dakile duk wata barazanar ta’addanci.

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 14 hours 44 minutes 33 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 16 hours 25 minutes 58 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com