Home Labarai Ghana ta Gargadi ‘yan kasarta kan zuwa Nijeriya

Ghana ta Gargadi ‘yan kasarta kan zuwa Nijeriya

Gwamnatin Ghana ta gargadi ‘yan kasarta kan balaguro zuwa babban birnin tarayyar Najeriya Abuja saboda matsalar tsaro.

Wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar ranar Laraba ta ce gargadin ya biyo bayan mawuyacin hali da ake ciki a babban birnin kasar da kuma umarnin da hukumomi Najeriya suka bayar na a rufe otal-otal da ke gidajen kwana.

Sanarwar ta ta bukaci ‘yan kasar Ghana da dole sai sun shiga birnin Abuja da su tabbaatar sun dauki matakin kariya da taka tsan-tsan, inda ma’aikatar za ta ci gaba da sanya ido kan yadda al’umara ke ganuna tare da bayar da bayanai ga jama’a idan lamarin ya daidaita.”

Ana yawan tafiye-tafiye tsakanin Ghana da Najeriya, manyan kasashe biyu mafi karfin tattalin arziki a yammacin Afirka.

Hakan na zuwa ne makonni bayan Amurka da wasu ofisoshin jakadancin kasashen waje sun yi gargadi game da tafiye-tafiye zuwa babban birnin Najeriya saboda barazanar ta’addanci.

Sai dai gwamnatin Najeriya ta roki ‘yan kasar da su kwantar da hankulansu tana mai tabbatar musu da cewa jami’an tsaro na kokarin dakile duk wata barazanar ta’addanci.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp