Home Labarai Sefeton ‘yan Sandan Nijeriya ya Magantu kan Umarnin Kotu

Sefeton ‘yan Sandan Nijeriya ya Magantu kan Umarnin Kotu

Babban Sufeton Ƴan Sandan Najeriya Usman Alkali Baba ya ce bai saɓa umarnin kotu ba sakamakon ba shi da masaniya kan wani hukunci da kotun ta yanke da ya shafi mayar da wani ɗan sanda kan aikinsa.

Wannan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ƴan sandan Najeriya CSP Olumuyiwa Adejobi, ya fitar inda tace babban sufeton ya ce an sallami ɗan sandan tun a 1992, shekaru kaɗan bayan shi kansa sufeton ya shiga aikin ɗan sanda.

Ya bayyana cewa hukunci na ƙarshe wanda kotu ta yanke a 2011 zamanin wani sufeto ne daban.

Sai dai Usman Alkali Baba ya ce ya bayar da umarni ga kwamishinan ƴan sanda wanda ke kula da ɓangaren shari’a da ya gudanar da bincike kan wannan zargin domin duba matsayar kotu da kuma ba sufeton shawarar da ta dace ta shari’a domin ɗaukar mataki.

A ɗazu ne Babbar Kotun Tarayyar Najeriya ta yanke wa Sufeton Ƴan sandan ƙasar hukuncin zaman gidan yari na wata uku.

Mai Shari’a Justice Mobolaji Olajuwon ce ta yanke hukuncin inda ta ce ya saɓa umarnin kotu kamar yadda kafar watsa labarai ta Channels a Najeriya ta ruwaito.

Tun farko dai wani ɗan sanda mai suna Patrick Okoli ne ya shigar da ƙara inda ya ce an yi masa ritaya ƙarfi da yaji a 1992 inda daga baya kotu ta bayar da umarnin a mayar da shi kan aikinsa tare da biyansa duka haƙƙoƙinsa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp