Home DUNIYA Buhari: Ana karkatar da wasu makaman da ake amfani da su a...

Buhari: Ana karkatar da wasu makaman da ake amfani da su a yakin dake gudana tsakanin Rasha da Ukraine zuwa Yankin Tafkin Chadi. 

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewar ana karkatar da wasu makaman da ake amfani da su a yakin dake gudana tsakanin Rasha da Ukraine zuwa Yankin Tafkin Chadi.

Buhari yace ya zama wajibi shugabannin dake yankin su tashi tsaye wajen daukar matakan da suka dace na dakile safarar kanana da manyan makaman dake kwarara zuwa yankin.

Shugaban yace babu tantama yakin Rasha da Ukraine tare da wasu tashe tashen hankulan dake ake fama da su a yankin Sahel sun taimaka wajen rura wutar rikicin Boko Haram a Tafkin Chadi.

Buhari yace duk da yake kasashen dake yankin sun yi kokari wajen dakile kaifin book haram da wasu kungiyoyi makamanta ta a yankin, har yanzu ana fuskantar barazanar yan ta’adda.

Shugaban wanda ya yaba da rawar da rundunar hadin kai ta kasashen guda 4 ke takawa wajen murkushe mayakan boko haram, ya bukace sojojin da su kara kaimi wajen fadada nasarorin da suke samu na kawar da duk wata barazanar da kasashen yankin ke fuskanta.

Buhari ya kuma bukaci kasashen Tafkin Chadin da su tashi tsaye wajen gudanar da ayyukan raya kasa wadanda zasu inganta rayuwar jama’ar su da kuma kare lafiyarsu.

Saboda haka shugaban ya bukaci aiwatar da shirin gina yankunan da aka kwato daga hannun mayakan book haram cikin gaggawa tare da samar da tsaro da kuma kayan more rayuwa.

Babban Sakataren dake kula da Hukumar Tafkin Chadi Ambasada Mamman Nuhu yace Najeriya ta bada kudin da ya zarce Dala miliyan 209 domin gudanar da ayyukan rundunar sojin hadin kan daga shekarar 2015 zuwa 2021.

Shugabannin da suka halarci taron sun hada da shugaban Nijar Bazoum Mohammed da shugaban Chadi Mahamat Idriss Deby da shugaban Benin Patrice Tallon da shugaban Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, Fautin Archange Touadera da shugaban majalisar rikon kwaryar Libya Mohammed al Menfi.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp