Home DUNIYA Wani Farmakin Hadin Gwiwa tsakano Congo da Burundi ya halaka mayaka 40

Wani Farmakin Hadin Gwiwa tsakano Congo da Burundi ya halaka mayaka 40

Rahotannin na bayyana An halaka ‘yan tawayen Burundi 40 a wani farmakin hadin gwiwa da sojojin Jamhuriyar Demokradiyyar Congo da Burundi suka kai a gabashin Congo.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Laftanar Marc Elongo-Kyondwa ya ce sojojin biyu “sun kai wani gagarumin farmaki” kan ‘yan tawayen Burundi.

Ya kara da cewa sojojin biyu sun fatattaki ‘yan tawayen FNL daga dukkan tsaunuka hudu da ke yankin Nabombi.

Sanarwar ta ruwaito Janar Ramazani Fundi, kwamandan ayyuka a yankin kudancin kasar Congo yana cewa, rundunar sojojin Congon ta yi kira ga al’ummar yankin da su ba da hadin kai ga sojojin, sannan kuma matasa su ware kansu daga kungiyoyin da ke dauke da makamai”.

Tun a watan Agusta, sojojin Burundin ke yaki da kungiyoyin masu dauke da makamai a yankin Kivu ta Kudu, a matsayin wani bangare na rundunar kungiyar kasashen gabashin Afirka (EAC).

A cikin watan Yuni, EAC ta yanke shawarar kafa rundunar yankin da ta kunshi sojojin Kenya da Uganda tare da sojojin Congo a arewacin Kivu da Ituri, da sojojin Sudan ta Kudu da ke Haut-Uele da kuma Burundi a kudancin Kivu.

Kinshasa da ke zargin Rwanda da goyon bayan ‘yan tawayen M23 a arewacin Kivu, ta ki yarda Kigali ta shiga cikin rundunar.

Kimanin shekaru 30 kenan gabashin Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo ke fama da kungiyoyin masu dauke da makamai, wasu na cikin gida, wasu kuma daga kasashe makwabta.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp