Home DUNIYA Wani Farmakin Hadin Gwiwa tsakano Congo da Burundi ya halaka mayaka 40

Wani Farmakin Hadin Gwiwa tsakano Congo da Burundi ya halaka mayaka 40

Rahotannin na bayyana An halaka ‘yan tawayen Burundi 40 a wani farmakin hadin gwiwa da sojojin Jamhuriyar Demokradiyyar Congo da Burundi suka kai a gabashin Congo.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Laftanar Marc Elongo-Kyondwa ya ce sojojin biyu “sun kai wani gagarumin farmaki” kan ‘yan tawayen Burundi.

Ya kara da cewa sojojin biyu sun fatattaki ‘yan tawayen FNL daga dukkan tsaunuka hudu da ke yankin Nabombi.

Sanarwar ta ruwaito Janar Ramazani Fundi, kwamandan ayyuka a yankin kudancin kasar Congo yana cewa, rundunar sojojin Congon ta yi kira ga al’ummar yankin da su ba da hadin kai ga sojojin, sannan kuma matasa su ware kansu daga kungiyoyin da ke dauke da makamai”.

Tun a watan Agusta, sojojin Burundin ke yaki da kungiyoyin masu dauke da makamai a yankin Kivu ta Kudu, a matsayin wani bangare na rundunar kungiyar kasashen gabashin Afirka (EAC).

A cikin watan Yuni, EAC ta yanke shawarar kafa rundunar yankin da ta kunshi sojojin Kenya da Uganda tare da sojojin Congo a arewacin Kivu da Ituri, da sojojin Sudan ta Kudu da ke Haut-Uele da kuma Burundi a kudancin Kivu.

Kinshasa da ke zargin Rwanda da goyon bayan ‘yan tawayen M23 a arewacin Kivu, ta ki yarda Kigali ta shiga cikin rundunar.

Kimanin shekaru 30 kenan gabashin Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo ke fama da kungiyoyin masu dauke da makamai, wasu na cikin gida, wasu kuma daga kasashe makwabta.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp