Home SIYASA Adeleke Ya karbi Rantsuwar Kama Aiki

Adeleke Ya karbi Rantsuwar Kama Aiki

An rantsar da Ademola Adeleke a matsayin sabon Gwamnan Jihar Osun, sakamakon nasarar da ya samu a zaben da akayi watannin da suka gabata.

Sabon gwamnan wanda nan take ya rufe asusun ajiyar jihar, ya bayyana aniyarsa ta bunkasa bangaren ilimi da tsaro da kula da lafiya da gina kayan more rayuwa, tare da sakin mara ga kananan hukumomi da kuma bangaren shari’a.

Adeleke ya kuma sanar da soke duk wasu nade naden da tsohon gwamnan yayi tun daga ranar 7 ga watan Yulin wannan shekara, cikinsu harda nada manyan sakatarorin gwamnati 30 da Oyetola yayi a makon jiya.

Sabon gwamnan ya kuma sauya sunan jihar daga ‘The State of Osun’ da ake kira, zuwa sunanta na assali, wato Jihar Osun.

Yayin bikin wanda ya samu halartar dan takarar shugaban kasar PDP Atiku Abukakar da gwamnonin jihohi da tsohon shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki, Gwamnan mai barin gado Adegboyega Oyetola yace ya barwa sabon gwamnan kundin da ya kai naira biliyan 14 a lalitar gwamnati.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp