Home SIYASA Adeleke Ya karbi Rantsuwar Kama Aiki

Adeleke Ya karbi Rantsuwar Kama Aiki

An rantsar da Ademola Adeleke a matsayin sabon Gwamnan Jihar Osun, sakamakon nasarar da ya samu a zaben da akayi watannin da suka gabata.

Sabon gwamnan wanda nan take ya rufe asusun ajiyar jihar, ya bayyana aniyarsa ta bunkasa bangaren ilimi da tsaro da kula da lafiya da gina kayan more rayuwa, tare da sakin mara ga kananan hukumomi da kuma bangaren shari’a.

Adeleke ya kuma sanar da soke duk wasu nade naden da tsohon gwamnan yayi tun daga ranar 7 ga watan Yulin wannan shekara, cikinsu harda nada manyan sakatarorin gwamnati 30 da Oyetola yayi a makon jiya.

Sabon gwamnan ya kuma sauya sunan jihar daga ‘The State of Osun’ da ake kira, zuwa sunanta na assali, wato Jihar Osun.

Yayin bikin wanda ya samu halartar dan takarar shugaban kasar PDP Atiku Abukakar da gwamnonin jihohi da tsohon shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki, Gwamnan mai barin gado Adegboyega Oyetola yace ya barwa sabon gwamnan kundin da ya kai naira biliyan 14 a lalitar gwamnati.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp