Home Labarai Jami’ai a Afrika ta kudu sun tabbatar da hallaka mutane da yawansu...

Jami’ai a Afrika ta kudu sun tabbatar da hallaka mutane da yawansu ya haura Dubu 7 a sassan Kasar,

Wasu sabbin alkaluma da rundunar ‘yan sandan Afrika ta kudu ta fitar sun nuna yadda aka kashe mutanen da yawansu ya haura dubu 7 a sassan kasar, wanda ke nuna karuwar laifuka da tashe-tashen hankula a kasar.

Rahoton da rundunar ‘yan sandan ta mikawa kwamitin majalisar kasar mai kula da laifuka a jiya laraba, ya nuna yadda aikata laifuka ya kai kololuwa tsakanin 1 ga watan Yulin da ya gabata zuwa 30 ga watan Satumba.

Rahoton ‘yan sandan ya bayyana cewa an samu karuwar aikata laifuka da kashe-kashe da akalla kashi 14 idan akwa kwatanta da yawan mutanen da aka kashe a irin lokacin cikin shekarar da ta gabata.

A irin wannan lokaci cikin shekarar 2021 makamantan tashe-tashen hankulan da rikice rikice da kuma kashe-kashen babu gaira babu dalili ya kai ga mutuwar mutane dubu 6 da 163 adadin da bai kai yadda aka samu a bana ba.

Akalla mata dubu guda ke cikin wadanda aka kashe cikin watannin 3 a Afrika ta kudu yayinda aka ci zarafin matan da yawansu ya haura dubu 13 sai kuma wasu dubu 1 da 277 da aka nufaci kashe su amma suka kubuta da kyar.

Rahoton rundunar ‘yan sandan ya nuna yadda aka yi garkuwa da mutanen da yawansu ya haura dubu 4000 cikin watannin 3 alkaluman da ke nuna yadda laifukan garkuwa suka karu da fin kashi 100 idan an kwatanta da bara.

Haka zalika laifukan cin zarafin mata da yara ta hanyar fyade ya karu da kashi 11 inda yanzu haka ake da kararraki fiye da dubu 10 gaban kotuna kan irin wadannan laifuka a sassan kasar cikin wannan lokaci.

Rahoton ya kuma bayyana yadda aka kashe yaran da yawansu ya kai 550 daga watan Aprilu zuwa Satumban shekarar nan a kasar ta Afrika ta kudu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp