Home Labarai Jami’ai a Afrika ta kudu sun tabbatar da hallaka mutane da yawansu...

Jami’ai a Afrika ta kudu sun tabbatar da hallaka mutane da yawansu ya haura Dubu 7 a sassan Kasar,

Wasu sabbin alkaluma da rundunar ‘yan sandan Afrika ta kudu ta fitar sun nuna yadda aka kashe mutanen da yawansu ya haura dubu 7 a sassan kasar, wanda ke nuna karuwar laifuka da tashe-tashen hankula a kasar.

Rahoton da rundunar ‘yan sandan ta mikawa kwamitin majalisar kasar mai kula da laifuka a jiya laraba, ya nuna yadda aikata laifuka ya kai kololuwa tsakanin 1 ga watan Yulin da ya gabata zuwa 30 ga watan Satumba.

Rahoton ‘yan sandan ya bayyana cewa an samu karuwar aikata laifuka da kashe-kashe da akalla kashi 14 idan akwa kwatanta da yawan mutanen da aka kashe a irin lokacin cikin shekarar da ta gabata.

A irin wannan lokaci cikin shekarar 2021 makamantan tashe-tashen hankulan da rikice rikice da kuma kashe-kashen babu gaira babu dalili ya kai ga mutuwar mutane dubu 6 da 163 adadin da bai kai yadda aka samu a bana ba.

Akalla mata dubu guda ke cikin wadanda aka kashe cikin watannin 3 a Afrika ta kudu yayinda aka ci zarafin matan da yawansu ya haura dubu 13 sai kuma wasu dubu 1 da 277 da aka nufaci kashe su amma suka kubuta da kyar.

Rahoton rundunar ‘yan sandan ya nuna yadda aka yi garkuwa da mutanen da yawansu ya haura dubu 4000 cikin watannin 3 alkaluman da ke nuna yadda laifukan garkuwa suka karu da fin kashi 100 idan an kwatanta da bara.

Haka zalika laifukan cin zarafin mata da yara ta hanyar fyade ya karu da kashi 11 inda yanzu haka ake da kararraki fiye da dubu 10 gaban kotuna kan irin wadannan laifuka a sassan kasar cikin wannan lokaci.

Rahoton ya kuma bayyana yadda aka kashe yaran da yawansu ya kai 550 daga watan Aprilu zuwa Satumban shekarar nan a kasar ta Afrika ta kudu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp