Home Labarai Jami’ai a Afrika ta kudu sun tabbatar da hallaka mutane da yawansu...

Jami’ai a Afrika ta kudu sun tabbatar da hallaka mutane da yawansu ya haura Dubu 7 a sassan Kasar,

Wasu sabbin alkaluma da rundunar ‘yan sandan Afrika ta kudu ta fitar sun nuna yadda aka kashe mutanen da yawansu ya haura dubu 7 a sassan kasar, wanda ke nuna karuwar laifuka da tashe-tashen hankula a kasar.

Rahoton da rundunar ‘yan sandan ta mikawa kwamitin majalisar kasar mai kula da laifuka a jiya laraba, ya nuna yadda aikata laifuka ya kai kololuwa tsakanin 1 ga watan Yulin da ya gabata zuwa 30 ga watan Satumba.

Rahoton ‘yan sandan ya bayyana cewa an samu karuwar aikata laifuka da kashe-kashe da akalla kashi 14 idan akwa kwatanta da yawan mutanen da aka kashe a irin lokacin cikin shekarar da ta gabata.

A irin wannan lokaci cikin shekarar 2021 makamantan tashe-tashen hankulan da rikice rikice da kuma kashe-kashen babu gaira babu dalili ya kai ga mutuwar mutane dubu 6 da 163 adadin da bai kai yadda aka samu a bana ba.

Akalla mata dubu guda ke cikin wadanda aka kashe cikin watannin 3 a Afrika ta kudu yayinda aka ci zarafin matan da yawansu ya haura dubu 13 sai kuma wasu dubu 1 da 277 da aka nufaci kashe su amma suka kubuta da kyar.

Rahoton rundunar ‘yan sandan ya nuna yadda aka yi garkuwa da mutanen da yawansu ya haura dubu 4000 cikin watannin 3 alkaluman da ke nuna yadda laifukan garkuwa suka karu da fin kashi 100 idan an kwatanta da bara.

Haka zalika laifukan cin zarafin mata da yara ta hanyar fyade ya karu da kashi 11 inda yanzu haka ake da kararraki fiye da dubu 10 gaban kotuna kan irin wadannan laifuka a sassan kasar cikin wannan lokaci.

Rahoton ya kuma bayyana yadda aka kashe yaran da yawansu ya kai 550 daga watan Aprilu zuwa Satumban shekarar nan a kasar ta Afrika ta kudu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp