Home Labarai Sefeton ‘yan Sandan Nijeriya ya Magantu kan Umarnin Kotu

Sefeton ‘yan Sandan Nijeriya ya Magantu kan Umarnin Kotu

Babban Sufeton Ƴan Sandan Najeriya Usman Alkali Baba ya ce bai saɓa umarnin kotu ba sakamakon ba shi da masaniya kan wani hukunci da kotun ta yanke da ya shafi mayar da wani ɗan sanda kan aikinsa.

Wannan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ƴan sandan Najeriya CSP Olumuyiwa Adejobi, ya fitar inda tace babban sufeton ya ce an sallami ɗan sandan tun a 1992, shekaru kaɗan bayan shi kansa sufeton ya shiga aikin ɗan sanda.

Ya bayyana cewa hukunci na ƙarshe wanda kotu ta yanke a 2011 zamanin wani sufeto ne daban.

Sai dai Usman Alkali Baba ya ce ya bayar da umarni ga kwamishinan ƴan sanda wanda ke kula da ɓangaren shari’a da ya gudanar da bincike kan wannan zargin domin duba matsayar kotu da kuma ba sufeton shawarar da ta dace ta shari’a domin ɗaukar mataki.

A ɗazu ne Babbar Kotun Tarayyar Najeriya ta yanke wa Sufeton Ƴan sandan ƙasar hukuncin zaman gidan yari na wata uku.

Mai Shari’a Justice Mobolaji Olajuwon ce ta yanke hukuncin inda ta ce ya saɓa umarnin kotu kamar yadda kafar watsa labarai ta Channels a Najeriya ta ruwaito.

Tun farko dai wani ɗan sanda mai suna Patrick Okoli ne ya shigar da ƙara inda ya ce an yi masa ritaya ƙarfi da yaji a 1992 inda daga baya kotu ta bayar da umarnin a mayar da shi kan aikinsa tare da biyansa duka haƙƙoƙinsa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp