Home General Jami’ar MAAUN, PRNigeria sunyi Hadin Gwiwa don Horas da Daliban Jami’ar Aikin...

Jami’ar MAAUN, PRNigeria sunyi Hadin Gwiwa don Horas da Daliban Jami’ar Aikin Jarida

Mamallaki kuma Wanda ya sama da Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nigeria wato (MAUUN) Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ya bukacin yin hadin Gwiwa da cibiyar PRNigeria domin horas da daliban Jami’ar sanin makamar aiki.
Farfesa Gwarzo ya bayyana hakan ne yayin da babban Shugaban kamfanin dillancin labarai na Image Merchants Promotion Limited masu wallafa jaridun PRNigeria da Economic Confidential, Malam Yushau Shuaib, ya jagoranci tawagar kamfani Wata ziyara a jihar Kano.
Farfesa Gwarzo ya godewa shugaban Kamfanin na IMPR bisa yadda ya bashi gudunmawar shawarwari, kalaman karin karfin Gwiwa wanda suka tallafa wajen cigaban Jami’ar.
PRNigeria na matsayin wata cibiya da ta dauki shekaru tana horas da dalibai musamman na tsangayar koyon aikin Jarida daga Jami’oi mabambanta.
Alhaji Shuaib ya bawa mamallakin Jami’ar tabbacin cewa cibiyar zata bawa Daliban makarantar horarwa mai inganci kuma matakin farko a fadin duniya.
Daga bisa Shuaib ya yaba da kokarin Gwarzo bisa tallafinsa ba ganin an kammala taron bada lambar karrama matasan Arewa mai lakabin Arewa 30 Under 30 Award wanda ya gudana a makon daya gabata.
Haka zalika ya yaba da kokarin gidauniyar Adamu Abubakar Gwarzo bisa yadda take bada tallafin jin kai ga masu karamin karfi a cikin Nijeriya dama sauran kasashen.
Farfesa Gwarzo, wanda ya samar da Jami’oin MAUUN a Nijeriya da Nijar, yanzu haka yana shirye -shiryen samar da wasu Jami’in Franco British International University a jihar Kaduna da Canadian University a birnin Abuja cikin shekarun 2023/2024.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp