Home General Dakarun Sojin Nijeriya sun Sake Hallaka ‘yan Bindiga a Jihar Kaduna

Dakarun Sojin Nijeriya sun Sake Hallaka ‘yan Bindiga a Jihar Kaduna

Dakarun sojin Nijeriya sun sake samun nasarar tarwatsa maboyar ‘yan bindiga a wani artabu da sukayi a Giwa dake jihar Kaduna.
Sojojin sun kuma samu nasarar ceto mata da kanana yara bayan tarwatsa maboyar.
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da Al’amurran cikin gida Samuel Aruwan ya fita.
Sanarwar tace Dakarun sojojin Nijeriya na musamman sun sake samun nasara kan ‘yan Ta’adda inda suka hallaka 9 bayan bata kashi a karamar hukumar Giwa ta Jihar.
A yayin da take bayyana rahoton tsaro Gwamnatin jihar kaduna tace dakarun su tarwatsa gungun ‘yan bindigar a maboyar su dake Rafin Sarki inda suka dakume biyar daga cikin su yayin da ragiwar suka tsere don tsira da rayukan su.
A wani bangare na gudanar da atisayen kawar da ‘yan Ta’addan dakarun na musamman sun sami nasarar tarwatsa maboyar su a Galadimawa inda dakarun suka hallaka hudu daga ciki gami da ceto mata da kananan yara da sukayi garkuwa da su.
Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya yaba da kokarin dakarun sojin bisa namijin kokarin da sukayi na ceto wadanda akayi garkuwa dasu.
Gwamnatin jihar ta kuma bukaci Al’umma da su cigaba da tallafawa da bayanan sirri kan maboyar ‘yan Ta’addan dama masu kai musu bayanan sirri ta wadannan lambobi waya:

09034000060
08170189999

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp