Home General Dakarun Sojin Nijeriya sun Sake Hallaka ‘yan Bindiga a Jihar Kaduna

Dakarun Sojin Nijeriya sun Sake Hallaka ‘yan Bindiga a Jihar Kaduna

Dakarun sojin Nijeriya sun sake samun nasarar tarwatsa maboyar ‘yan bindiga a wani artabu da sukayi a Giwa dake jihar Kaduna.
Sojojin sun kuma samu nasarar ceto mata da kanana yara bayan tarwatsa maboyar.
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da Al’amurran cikin gida Samuel Aruwan ya fita.
Sanarwar tace Dakarun sojojin Nijeriya na musamman sun sake samun nasara kan ‘yan Ta’adda inda suka hallaka 9 bayan bata kashi a karamar hukumar Giwa ta Jihar.
A yayin da take bayyana rahoton tsaro Gwamnatin jihar kaduna tace dakarun su tarwatsa gungun ‘yan bindigar a maboyar su dake Rafin Sarki inda suka dakume biyar daga cikin su yayin da ragiwar suka tsere don tsira da rayukan su.
A wani bangare na gudanar da atisayen kawar da ‘yan Ta’addan dakarun na musamman sun sami nasarar tarwatsa maboyar su a Galadimawa inda dakarun suka hallaka hudu daga ciki gami da ceto mata da kananan yara da sukayi garkuwa da su.
Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya yaba da kokarin dakarun sojin bisa namijin kokarin da sukayi na ceto wadanda akayi garkuwa dasu.
Gwamnatin jihar ta kuma bukaci Al’umma da su cigaba da tallafawa da bayanan sirri kan maboyar ‘yan Ta’addan dama masu kai musu bayanan sirri ta wadannan lambobi waya:

09034000060
08170189999

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp