Home General Dakarun Sojin Nijeriya sun Sake Hallaka ‘yan Bindiga a Jihar Kaduna

Dakarun Sojin Nijeriya sun Sake Hallaka ‘yan Bindiga a Jihar Kaduna

Dakarun sojin Nijeriya sun sake samun nasarar tarwatsa maboyar ‘yan bindiga a wani artabu da sukayi a Giwa dake jihar Kaduna.
Sojojin sun kuma samu nasarar ceto mata da kanana yara bayan tarwatsa maboyar.
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da Al’amurran cikin gida Samuel Aruwan ya fita.
Sanarwar tace Dakarun sojojin Nijeriya na musamman sun sake samun nasara kan ‘yan Ta’adda inda suka hallaka 9 bayan bata kashi a karamar hukumar Giwa ta Jihar.
A yayin da take bayyana rahoton tsaro Gwamnatin jihar kaduna tace dakarun su tarwatsa gungun ‘yan bindigar a maboyar su dake Rafin Sarki inda suka dakume biyar daga cikin su yayin da ragiwar suka tsere don tsira da rayukan su.
A wani bangare na gudanar da atisayen kawar da ‘yan Ta’addan dakarun na musamman sun sami nasarar tarwatsa maboyar su a Galadimawa inda dakarun suka hallaka hudu daga ciki gami da ceto mata da kananan yara da sukayi garkuwa da su.
Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya yaba da kokarin dakarun sojin bisa namijin kokarin da sukayi na ceto wadanda akayi garkuwa dasu.
Gwamnatin jihar ta kuma bukaci Al’umma da su cigaba da tallafawa da bayanan sirri kan maboyar ‘yan Ta’addan dama masu kai musu bayanan sirri ta wadannan lambobi waya:

09034000060
08170189999

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp