Home General Jami’ar MAAUN, PRNigeria sunyi Hadin Gwiwa don Horas da Daliban Jami’ar Aikin...

Jami’ar MAAUN, PRNigeria sunyi Hadin Gwiwa don Horas da Daliban Jami’ar Aikin Jarida

Mamallaki kuma Wanda ya sama da Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nigeria wato (MAUUN) Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ya bukacin yin hadin Gwiwa da cibiyar PRNigeria domin horas da daliban Jami’ar sanin makamar aiki.
Farfesa Gwarzo ya bayyana hakan ne yayin da babban Shugaban kamfanin dillancin labarai na Image Merchants Promotion Limited masu wallafa jaridun PRNigeria da Economic Confidential, Malam Yushau Shuaib, ya jagoranci tawagar kamfani Wata ziyara a jihar Kano.
Farfesa Gwarzo ya godewa shugaban Kamfanin na IMPR bisa yadda ya bashi gudunmawar shawarwari, kalaman karin karfin Gwiwa wanda suka tallafa wajen cigaban Jami’ar.
PRNigeria na matsayin wata cibiya da ta dauki shekaru tana horas da dalibai musamman na tsangayar koyon aikin Jarida daga Jami’oi mabambanta.
Alhaji Shuaib ya bawa mamallakin Jami’ar tabbacin cewa cibiyar zata bawa Daliban makarantar horarwa mai inganci kuma matakin farko a fadin duniya.
Daga bisa Shuaib ya yaba da kokarin Gwarzo bisa tallafinsa ba ganin an kammala taron bada lambar karrama matasan Arewa mai lakabin Arewa 30 Under 30 Award wanda ya gudana a makon daya gabata.
Haka zalika ya yaba da kokarin gidauniyar Adamu Abubakar Gwarzo bisa yadda take bada tallafin jin kai ga masu karamin karfi a cikin Nijeriya dama sauran kasashen.
Farfesa Gwarzo, wanda ya samar da Jami’oin MAUUN a Nijeriya da Nijar, yanzu haka yana shirye -shiryen samar da wasu Jami’in Franco British International University a jihar Kaduna da Canadian University a birnin Abuja cikin shekarun 2023/2024.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp