Home General Jami’ar MAAUN, PRNigeria sunyi Hadin Gwiwa don Horas da Daliban Jami’ar Aikin...

Jami’ar MAAUN, PRNigeria sunyi Hadin Gwiwa don Horas da Daliban Jami’ar Aikin Jarida

Mamallaki kuma Wanda ya sama da Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nigeria wato (MAUUN) Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ya bukacin yin hadin Gwiwa da cibiyar PRNigeria domin horas da daliban Jami’ar sanin makamar aiki.
Farfesa Gwarzo ya bayyana hakan ne yayin da babban Shugaban kamfanin dillancin labarai na Image Merchants Promotion Limited masu wallafa jaridun PRNigeria da Economic Confidential, Malam Yushau Shuaib, ya jagoranci tawagar kamfani Wata ziyara a jihar Kano.
Farfesa Gwarzo ya godewa shugaban Kamfanin na IMPR bisa yadda ya bashi gudunmawar shawarwari, kalaman karin karfin Gwiwa wanda suka tallafa wajen cigaban Jami’ar.
PRNigeria na matsayin wata cibiya da ta dauki shekaru tana horas da dalibai musamman na tsangayar koyon aikin Jarida daga Jami’oi mabambanta.
Alhaji Shuaib ya bawa mamallakin Jami’ar tabbacin cewa cibiyar zata bawa Daliban makarantar horarwa mai inganci kuma matakin farko a fadin duniya.
Daga bisa Shuaib ya yaba da kokarin Gwarzo bisa tallafinsa ba ganin an kammala taron bada lambar karrama matasan Arewa mai lakabin Arewa 30 Under 30 Award wanda ya gudana a makon daya gabata.
Haka zalika ya yaba da kokarin gidauniyar Adamu Abubakar Gwarzo bisa yadda take bada tallafin jin kai ga masu karamin karfi a cikin Nijeriya dama sauran kasashen.
Farfesa Gwarzo, wanda ya samar da Jami’oin MAUUN a Nijeriya da Nijar, yanzu haka yana shirye -shiryen samar da wasu Jami’in Franco British International University a jihar Kaduna da Canadian University a birnin Abuja cikin shekarun 2023/2024.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp