Home General Jami’ar MAAUN, PRNigeria sunyi Hadin Gwiwa don Horas da Daliban Jami’ar Aikin...

Jami’ar MAAUN, PRNigeria sunyi Hadin Gwiwa don Horas da Daliban Jami’ar Aikin Jarida

Mamallaki kuma Wanda ya sama da Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nigeria wato (MAUUN) Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ya bukacin yin hadin Gwiwa da cibiyar PRNigeria domin horas da daliban Jami’ar sanin makamar aiki.
Farfesa Gwarzo ya bayyana hakan ne yayin da babban Shugaban kamfanin dillancin labarai na Image Merchants Promotion Limited masu wallafa jaridun PRNigeria da Economic Confidential, Malam Yushau Shuaib, ya jagoranci tawagar kamfani Wata ziyara a jihar Kano.
Farfesa Gwarzo ya godewa shugaban Kamfanin na IMPR bisa yadda ya bashi gudunmawar shawarwari, kalaman karin karfin Gwiwa wanda suka tallafa wajen cigaban Jami’ar.
PRNigeria na matsayin wata cibiya da ta dauki shekaru tana horas da dalibai musamman na tsangayar koyon aikin Jarida daga Jami’oi mabambanta.
Alhaji Shuaib ya bawa mamallakin Jami’ar tabbacin cewa cibiyar zata bawa Daliban makarantar horarwa mai inganci kuma matakin farko a fadin duniya.
Daga bisa Shuaib ya yaba da kokarin Gwarzo bisa tallafinsa ba ganin an kammala taron bada lambar karrama matasan Arewa mai lakabin Arewa 30 Under 30 Award wanda ya gudana a makon daya gabata.
Haka zalika ya yaba da kokarin gidauniyar Adamu Abubakar Gwarzo bisa yadda take bada tallafin jin kai ga masu karamin karfi a cikin Nijeriya dama sauran kasashen.
Farfesa Gwarzo, wanda ya samar da Jami’oin MAUUN a Nijeriya da Nijar, yanzu haka yana shirye -shiryen samar da wasu Jami’in Franco British International University a jihar Kaduna da Canadian University a birnin Abuja cikin shekarun 2023/2024.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp