Home General Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Tarayya ta bayar da Umarnin bude sabuwar gadar Niger

Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Tarayya ta bayar da Umarnin bude sabuwar gadar Niger

 Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta bada umarnin bude gadar domin yin amfani da ita na tsawon wata guda farawa da daren Alhamis.
Ministan Ayyuka Babatunde Fashola SAN, ne ya bayyana hakan yayin da yake kaddamar da gadar don amfani da ita wajen bukukuwan kirsimeti da sabuwar shekara.
Fasola a lokacin dake tafiya kan gadar ya bukaci matuka da suyi amfani da ita yadda ya kamata cikin nutsuwa kada suyi abinda zasu kawo tsaiko ga musabbabin samar da ita.
Ministan yace dalilin shugaban kasa Muhammadu Buhari na kammala aiki shine domin tseratar da rayukan Al’umma da kuma kawar da talauci wanda ke aukuwa sakamakon bata sa’oi cikin cunkoso akan tsohuwar gadar Farko ta Niger.
Ya kuma tabbatar da cewa samar da gadar zai taimaka wajen rage wahalhalun da matuka ke sha cikin cunkosu a yayin bukukuwan na kirsimeti da karshen shekara.
Yace gadar bazata zama mai amfani ba muddi ba’a bi da ita yadda ya kamata ba.
Daga bisani Fasola ya ce an bude gadar a hukumance daga rana
Alhamis 15 ga Disambar 2022 da misalin 12:01am zuwa 15 ga watan Janairun 2023

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp