Home General Kwamandan MNJTF ya mika Motocin yaki ga Dakarun dake Kirawa

Kwamandan MNJTF ya mika Motocin yaki ga Dakarun dake Kirawa

Kwamandan MNJTF ya mika Motocin yaki ga Dakarun dake Kirawa.
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da shugaban sashen yada labarai na rundunar a N’Djamena dake Chadi laftanal Kanal KAMARUDEEN ADEGOKE, mai dauke da kwanan watan 15 ga watan Disambar 2022.
Sanarwar tace kwamandan rundunar hadin Gwiwar ta MNJTF, Manjo Janar Abdul Khalifa Ibrahim daya sami rakiyar mataimakin sa Birgediya Janal Assouala Blama da kwamandan sashe na 1 na rundunar a kamaru kanal Tiokap Loti yayin ziyarar ta aiki Da suka kai Shalkwatar Rundunar sojin a kirawa dake iyakar Nijeriya da Kamaru a yankin jihar Borno dake Nijeriya a ranar laraba.
Sun sami tarbar Babban kwamandan runduna ta bakwai 7 (GOC) Manjo Janar W Shaibu, bayan bikin tarbar soji ta Al’ada manjo Janar Sha’aibu ya yaba bisa Motocin yaki da aka bawa rundunar kirar ( Toyota Buffalo Hillux fitted for Combat).
Ya yaba ga shugaban Rundunar Sojin Nijeriya Janar Lucky Irabor da shugaban sojin kasa Laftanal Janal F. Yahaya da suka samar da motocin domin inganta ayyukan rundunar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp