Home General Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Tarayya ta bayar da Umarnin bude sabuwar gadar Niger

Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Tarayya ta bayar da Umarnin bude sabuwar gadar Niger

 Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta bada umarnin bude gadar domin yin amfani da ita na tsawon wata guda farawa da daren Alhamis.
Ministan Ayyuka Babatunde Fashola SAN, ne ya bayyana hakan yayin da yake kaddamar da gadar don amfani da ita wajen bukukuwan kirsimeti da sabuwar shekara.
Fasola a lokacin dake tafiya kan gadar ya bukaci matuka da suyi amfani da ita yadda ya kamata cikin nutsuwa kada suyi abinda zasu kawo tsaiko ga musabbabin samar da ita.
Ministan yace dalilin shugaban kasa Muhammadu Buhari na kammala aiki shine domin tseratar da rayukan Al’umma da kuma kawar da talauci wanda ke aukuwa sakamakon bata sa’oi cikin cunkoso akan tsohuwar gadar Farko ta Niger.
Ya kuma tabbatar da cewa samar da gadar zai taimaka wajen rage wahalhalun da matuka ke sha cikin cunkosu a yayin bukukuwan na kirsimeti da karshen shekara.
Yace gadar bazata zama mai amfani ba muddi ba’a bi da ita yadda ya kamata ba.
Daga bisani Fasola ya ce an bude gadar a hukumance daga rana
Alhamis 15 ga Disambar 2022 da misalin 12:01am zuwa 15 ga watan Janairun 2023

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp