‘Yan sanda sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan da ake nema ruwa a jallo a jihar katsina

‘Yan sanda sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan da ake nema ruwa a jallo a jihar katsina,
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da kakakin rundunar SP GAMBO ISAH, ANIPR ya fita a madadin kwamishinan ‘yan sanda jihar, sanarwa tace ‘yan ta’addan sun hadar da Na-Iraqi, Na-Masari.
Sanarwa mai dauke da kwanan watan 13 ga watan Disambar 2022 tace da misalin karfe 7:30 jami’an ‘yansan sun sami kiran cewa ‘yan bindiga sun tasamma yankin Sokoto – Rima Quarters dake karamar hukumar Dutsinma a jihar Katsina suna harbi kan mai uwa da wabi da bindiga kirar AK47, da nufin yin garkuwa da wani mazaunin yankin.
Babu bata lokaci dakarun dake lura da yankin suka garzaya wurin domin kai dauki, da isar su suka fara musayar wuta da ‘yan bindigar suka kuma sami nasarar hallaka 2 daga cikin su wadanda kuma suna jadawalin wadanda ake nema ruwa a jallo da suka hadar da Abu Na-Iraqi da Abu Na-Masari suka kuma sami nasarar kwato bindiga kirar AK47.
Jami’an ‘Yan sanda sun shiga bincike domin gano wadan suka tsere da raunukan harbi a jikin su.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 25 minutes 34 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 6 minutes 59 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com