Home General Gwamnatin Nijeriya ta Ayyana hutun Kirsimeti da Sabuwar Shekara

Gwamnatin Nijeriya ta Ayyana hutun Kirsimeti da Sabuwar Shekara

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta sanya ranar litinin 26 da Talata 27 ga watan Disambar 2022, da litinin 2 ga Janairun 2023 a matsayin ranar Hutun bukukuwan kirsimeti da sabuwar shekara a kasar.
Ministan cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, ne ya bayyana hakan a madadin Gwamnatin Tarayyar Nijeriya, inda ya taya daukacin mabiya Yesu Almasihu dake kasar da kasashen ketare murnan bikin kirsimeti da sabuwar shekara.
Ya bukaci kiristoci da suyi koyi da Yesu, wajen nuna kauna da Soyayya, tausayin Al’umma, zaman lafiya wannan itace hanyar nuna kauna da murnar haihuwar sa.
Ya jaddada cewa zaman lafiya da tsaro sune ginshikin inganta tattalin arzikin da cigaba, ya bukaci kiristoci da Dukkannin daukacin Al’ummar Nijeriya da suyi amfani da lokacin wajen yiwa kasar Addu’oin kawar da matsalolin rashin tsaron daya Addabi kasar.
Daga bisani ya bukaci Al’ummar kasar su mayar da hankali a fannin tsaro ta hanyar fallasa dukkan wani abu da basu yadda da shi ba

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp