Home General Za’a Nada Ambasada Ahmad Rufa’i Matsayin Sabon ‘Sardaunan Katsina’

Za’a Nada Ambasada Ahmad Rufa’i Matsayin Sabon ‘Sardaunan Katsina’

Majalisar Masarautar Katsina ta sanarwar da tsare-tsare nadin sabon sardaunan Katsina, Ambassador Ahmed Rufa’i Abubakar.
Guda cikin Mambobin Majalisar ne ya bayyanawa PRNigeria cewa sabon sardaunan wanda shine babban Daraktan hukumar tsaro da bayanan sirri ta Nijeriya (NIA) wanda za’ayi bikin ranar 31 ga watan Disambar 2022 a fadar Mai Martaba sarkin katsina dake Jihar.
Majalisar ta fayyace cewa sarautar ta sardauna ana alakanta ta ne da Tsohon Firaministan jihar Arewa Sir Ahmadu Bello, wanda ba mutum ne zai bukaci cewa a nadashi ba, Majalisar tace ana duba jajircewa, da farin jini da kuma cancantar mutum, gami da hangen nesa na mai martaba sarkin Katsina Alhaji (Dr) Abdulmumini Kabir Usman, CFR, wanda ya aro Sardaunan daga Masarautar sokkwato domin kara kare ta a tarihi.
Shirye-shiryen nadin dai zai fara ne da wasan dawaki a ranar 27 ga watan December, 2022 a Rubicon Polo and Resorts Centre, Idu, Abuja, sai kuma wasan Golf da zai biyo baya a filin wasan Golf na Katsina a 28 ga watan December.
Daga ranar 29 zuwa 30 ga watan Disambar kuwa za’a gudanar taro mai taken Al’adu da martabarsu, da batutuwa kan tarihin Katsina, a babban daki taro na Katsina Motel.
Yayin da mai martaba sarkin Katsina Alhaji Abdulmuminu Kabir Usman CFR, zai jagoranci nadin a fadarsa da karfe 10 na safe.
PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp