Home General Za’a Nada Ambasada Ahmad Rufa’i Matsayin Sabon ‘Sardaunan Katsina’

Za’a Nada Ambasada Ahmad Rufa’i Matsayin Sabon ‘Sardaunan Katsina’

Majalisar Masarautar Katsina ta sanarwar da tsare-tsare nadin sabon sardaunan Katsina, Ambassador Ahmed Rufa’i Abubakar.
Guda cikin Mambobin Majalisar ne ya bayyanawa PRNigeria cewa sabon sardaunan wanda shine babban Daraktan hukumar tsaro da bayanan sirri ta Nijeriya (NIA) wanda za’ayi bikin ranar 31 ga watan Disambar 2022 a fadar Mai Martaba sarkin katsina dake Jihar.
Majalisar ta fayyace cewa sarautar ta sardauna ana alakanta ta ne da Tsohon Firaministan jihar Arewa Sir Ahmadu Bello, wanda ba mutum ne zai bukaci cewa a nadashi ba, Majalisar tace ana duba jajircewa, da farin jini da kuma cancantar mutum, gami da hangen nesa na mai martaba sarkin Katsina Alhaji (Dr) Abdulmumini Kabir Usman, CFR, wanda ya aro Sardaunan daga Masarautar sokkwato domin kara kare ta a tarihi.
Shirye-shiryen nadin dai zai fara ne da wasan dawaki a ranar 27 ga watan December, 2022 a Rubicon Polo and Resorts Centre, Idu, Abuja, sai kuma wasan Golf da zai biyo baya a filin wasan Golf na Katsina a 28 ga watan December.
Daga ranar 29 zuwa 30 ga watan Disambar kuwa za’a gudanar taro mai taken Al’adu da martabarsu, da batutuwa kan tarihin Katsina, a babban daki taro na Katsina Motel.
Yayin da mai martaba sarkin Katsina Alhaji Abdulmuminu Kabir Usman CFR, zai jagoranci nadin a fadarsa da karfe 10 na safe.
PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp