Home General Za’a Nada Ambasada Ahmad Rufa’i Matsayin Sabon ‘Sardaunan Katsina’

Za’a Nada Ambasada Ahmad Rufa’i Matsayin Sabon ‘Sardaunan Katsina’

Majalisar Masarautar Katsina ta sanarwar da tsare-tsare nadin sabon sardaunan Katsina, Ambassador Ahmed Rufa’i Abubakar.
Guda cikin Mambobin Majalisar ne ya bayyanawa PRNigeria cewa sabon sardaunan wanda shine babban Daraktan hukumar tsaro da bayanan sirri ta Nijeriya (NIA) wanda za’ayi bikin ranar 31 ga watan Disambar 2022 a fadar Mai Martaba sarkin katsina dake Jihar.
Majalisar ta fayyace cewa sarautar ta sardauna ana alakanta ta ne da Tsohon Firaministan jihar Arewa Sir Ahmadu Bello, wanda ba mutum ne zai bukaci cewa a nadashi ba, Majalisar tace ana duba jajircewa, da farin jini da kuma cancantar mutum, gami da hangen nesa na mai martaba sarkin Katsina Alhaji (Dr) Abdulmumini Kabir Usman, CFR, wanda ya aro Sardaunan daga Masarautar sokkwato domin kara kare ta a tarihi.
Shirye-shiryen nadin dai zai fara ne da wasan dawaki a ranar 27 ga watan December, 2022 a Rubicon Polo and Resorts Centre, Idu, Abuja, sai kuma wasan Golf da zai biyo baya a filin wasan Golf na Katsina a 28 ga watan December.
Daga ranar 29 zuwa 30 ga watan Disambar kuwa za’a gudanar taro mai taken Al’adu da martabarsu, da batutuwa kan tarihin Katsina, a babban daki taro na Katsina Motel.
Yayin da mai martaba sarkin Katsina Alhaji Abdulmuminu Kabir Usman CFR, zai jagoranci nadin a fadarsa da karfe 10 na safe.
PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp