Home General Za’a Nada Ambasada Ahmad Rufa’i Matsayin Sabon ‘Sardaunan Katsina’

Za’a Nada Ambasada Ahmad Rufa’i Matsayin Sabon ‘Sardaunan Katsina’

Majalisar Masarautar Katsina ta sanarwar da tsare-tsare nadin sabon sardaunan Katsina, Ambassador Ahmed Rufa’i Abubakar.
Guda cikin Mambobin Majalisar ne ya bayyanawa PRNigeria cewa sabon sardaunan wanda shine babban Daraktan hukumar tsaro da bayanan sirri ta Nijeriya (NIA) wanda za’ayi bikin ranar 31 ga watan Disambar 2022 a fadar Mai Martaba sarkin katsina dake Jihar.
Majalisar ta fayyace cewa sarautar ta sardauna ana alakanta ta ne da Tsohon Firaministan jihar Arewa Sir Ahmadu Bello, wanda ba mutum ne zai bukaci cewa a nadashi ba, Majalisar tace ana duba jajircewa, da farin jini da kuma cancantar mutum, gami da hangen nesa na mai martaba sarkin Katsina Alhaji (Dr) Abdulmumini Kabir Usman, CFR, wanda ya aro Sardaunan daga Masarautar sokkwato domin kara kare ta a tarihi.
Shirye-shiryen nadin dai zai fara ne da wasan dawaki a ranar 27 ga watan December, 2022 a Rubicon Polo and Resorts Centre, Idu, Abuja, sai kuma wasan Golf da zai biyo baya a filin wasan Golf na Katsina a 28 ga watan December.
Daga ranar 29 zuwa 30 ga watan Disambar kuwa za’a gudanar taro mai taken Al’adu da martabarsu, da batutuwa kan tarihin Katsina, a babban daki taro na Katsina Motel.
Yayin da mai martaba sarkin Katsina Alhaji Abdulmuminu Kabir Usman CFR, zai jagoranci nadin a fadarsa da karfe 10 na safe.
PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp