Home General Dakarun sojin Saman Nijeriya sun Halaka ‘Ya Ta’adda sama da 60 a...

Dakarun sojin Saman Nijeriya sun Halaka ‘Ya Ta’adda sama da 60 a jihar Zamfara

Dakarun sojojin saman Najeriya sun yi luguden wuta da jirage kan sansanin ‘yan bindiga dake kauyen Mutumji a karamar hukumar Maru ta Jihar Zamfara, abinda yayi sanadiyar kashe hallaka akalla 60 daga cikinsu.

Rahotanni sun ce daga cikin mutanen da harin ya ritsa da su harda mata da kuma yara wadanda suke yankin lokacin da harin.

Bayanai sun ce harin ya biyo bayan koken da mazauna kauyukan Malele da Ruwan Tofa da ‘yan awaki suka gabatar na cewar ‘yan bindigar sun farwa garuruwansu, abinda ya sa sojojin daukar matakin kai musu dauki ta sama.

Wani mazaunin yankin ya tabbatar da aukuwar lamarin, yayin da ya kuma bayyana mana cewar yayin kai daukin ta sama sojojin cikin kuskure sun hallaka wasu daga cikin abokan aikin su dake kai hari ta kasa.

Majiyar tace yayin da ake wannan, wasu yan bindigar sun yiwa tawagar sojoji kwantar bauna inda suka kaiwa motocinsu guda 3 hari a yankin.

Jihar Zamfara na ci gaba da fuskantar munanan hare hare daga ‘yan bindiga wadanda ke sanyawa garuruwa haraji domin hana kai musu hari.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp