Home General Gwamnatin Nijeriya ta Ayyana hutun Kirsimeti da Sabuwar Shekara

Gwamnatin Nijeriya ta Ayyana hutun Kirsimeti da Sabuwar Shekara

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta sanya ranar litinin 26 da Talata 27 ga watan Disambar 2022, da litinin 2 ga Janairun 2023 a matsayin ranar Hutun bukukuwan kirsimeti da sabuwar shekara a kasar.
Ministan cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, ne ya bayyana hakan a madadin Gwamnatin Tarayyar Nijeriya, inda ya taya daukacin mabiya Yesu Almasihu dake kasar da kasashen ketare murnan bikin kirsimeti da sabuwar shekara.
Ya bukaci kiristoci da suyi koyi da Yesu, wajen nuna kauna da Soyayya, tausayin Al’umma, zaman lafiya wannan itace hanyar nuna kauna da murnar haihuwar sa.
Ya jaddada cewa zaman lafiya da tsaro sune ginshikin inganta tattalin arzikin da cigaba, ya bukaci kiristoci da Dukkannin daukacin Al’ummar Nijeriya da suyi amfani da lokacin wajen yiwa kasar Addu’oin kawar da matsalolin rashin tsaron daya Addabi kasar.
Daga bisani ya bukaci Al’ummar kasar su mayar da hankali a fannin tsaro ta hanyar fallasa dukkan wani abu da basu yadda da shi ba

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp