Home General Gwamnatin Nijeriya ta Ayyana hutun Kirsimeti da Sabuwar Shekara

Gwamnatin Nijeriya ta Ayyana hutun Kirsimeti da Sabuwar Shekara

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta sanya ranar litinin 26 da Talata 27 ga watan Disambar 2022, da litinin 2 ga Janairun 2023 a matsayin ranar Hutun bukukuwan kirsimeti da sabuwar shekara a kasar.
Ministan cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, ne ya bayyana hakan a madadin Gwamnatin Tarayyar Nijeriya, inda ya taya daukacin mabiya Yesu Almasihu dake kasar da kasashen ketare murnan bikin kirsimeti da sabuwar shekara.
Ya bukaci kiristoci da suyi koyi da Yesu, wajen nuna kauna da Soyayya, tausayin Al’umma, zaman lafiya wannan itace hanyar nuna kauna da murnar haihuwar sa.
Ya jaddada cewa zaman lafiya da tsaro sune ginshikin inganta tattalin arzikin da cigaba, ya bukaci kiristoci da Dukkannin daukacin Al’ummar Nijeriya da suyi amfani da lokacin wajen yiwa kasar Addu’oin kawar da matsalolin rashin tsaron daya Addabi kasar.
Daga bisani ya bukaci Al’ummar kasar su mayar da hankali a fannin tsaro ta hanyar fallasa dukkan wani abu da basu yadda da shi ba

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp