Home General Buhari zai Kaddamar da sabbin Ayyuka a Jihar Kogi

Buhari zai Kaddamar da sabbin Ayyuka a Jihar Kogi

Gwamnatin Jihar Kogi dake arewa ta tsakiyar Nijeriya ta ayyana ranar Alhamis a matsayin hutu, saboda ziyarar da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari zai kai Jihar.
Gwamnatin ta ce Buhari zai kai ziyarar ce don bude wasu ayyuka da Gwamnan Jihar, Yahaya Bello ya kammala.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yada Labaran Jihar, Kingsley Fanwo, ya fitar a ranar Lahadi a Lokoja, babban birnin Jihar.
Gwamnatin jihar ta bukaci al’ummar da su yi fitar farin dango don tarbar Shugaba Buhari.
Kazalika, Gwamnatin ta bukaci kungiyoyin kwadago da masu zaman kansu da jami’an tsaro su tabbatar da zaman lafiya ya wakana a yayin ziyarar ta Buhari.
Buhari dai na ci gaba da ziyartar jihohin Najeriya don kaddamar da ayyuka.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp