Home General Gwamnatin Jihar Kano zata Kaddamar da Sabuwar Tashar wutar Lantarki a jihar

Gwamnatin Jihar Kano zata Kaddamar da Sabuwar Tashar wutar Lantarki a jihar

Gwamnatin Jihar Kano a Arewacin Najeriya ta ce nan da makwanni 6 za a kammala aikin tashar samar da wutar lantarki ta Tiga mai karfin mega watt 10
Gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje ya ba da tabbacin ne lokacin ziyarar ganin yadda aikin tashar samar da wutar lantarki na Tiga da na samar da ruwa da ke Tamburawa yake gudana.
Cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran gwamnan Malam Abba Anwar ya fitar a jihar Kano, ta ce tashar samar da wutar lantarkin a matakin gwaji kafin kaddamarwa.
Gwamnan ya kuma yabawa kamfanin samar da hasken wutar lantarki mallakin jihar KHEDCO da kamfanin da aka baiwa kwangilar aiki da kuma sauran masu ruwa da tsaki.
A cewar gwamnan na da makwanni kadan wutar lantarkin na Tiga za a jona shi da tashar samar da ruwa ta Tamburawa , yana mai bada tabbacin cewa zai yi iyakar kokari dan ganin ya bar tarihi a dukkanin bangarorin ciyar da al’umma gaba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp