Home DUNIYA Ma’aikatar Tsaron Jamhuriyyar Nijar ta tabbatar da Mutuwar Mutane 3 sakamakon Hadarin...

Ma’aikatar Tsaron Jamhuriyyar Nijar ta tabbatar da Mutuwar Mutane 3 sakamakon Hadarin Jirgin Yaki

Wani jirgin soji mai saukar angulu kirar Mi-17, ya yi hadadi a filin sauka da tashin jiragen saman birnin Yamai da ke jamhuriyar Nijar, inda mutane uku da ke cikinsa suka rasa rayukansu nan take.

Ma’aikatar tsaron kasar ta ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 10 da mintuna 40 na safe.

Wata sanarwa da ma’aikatar da ma’aikatar tsaron kasar ta fitar a tsakiyar ranar litinin, ta ce jirgin ya yi hadari ne lokacin da yake sauka, bayan dawowa daga atisayen bayar da horo, kuma wadanda suka rasa rayukansu sun hadar da babban hafsan soji daya, da karamin hafsa daya sai kuma wanda ke horas da su dan asalin wata kasa ta kerare.

Ma’aikatar tsaron ta ce tuni ta kaddamar da bincike domin gano musababbin wannan hadari, tare da bayyana juyayi dangane da faruwar lamarin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp