Home DUNIYA Ma’aikatar Tsaron Jamhuriyyar Nijar ta tabbatar da Mutuwar Mutane 3 sakamakon Hadarin...

Ma’aikatar Tsaron Jamhuriyyar Nijar ta tabbatar da Mutuwar Mutane 3 sakamakon Hadarin Jirgin Yaki

Wani jirgin soji mai saukar angulu kirar Mi-17, ya yi hadadi a filin sauka da tashin jiragen saman birnin Yamai da ke jamhuriyar Nijar, inda mutane uku da ke cikinsa suka rasa rayukansu nan take.

Ma’aikatar tsaron kasar ta ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 10 da mintuna 40 na safe.

Wata sanarwa da ma’aikatar da ma’aikatar tsaron kasar ta fitar a tsakiyar ranar litinin, ta ce jirgin ya yi hadari ne lokacin da yake sauka, bayan dawowa daga atisayen bayar da horo, kuma wadanda suka rasa rayukansu sun hadar da babban hafsan soji daya, da karamin hafsa daya sai kuma wanda ke horas da su dan asalin wata kasa ta kerare.

Ma’aikatar tsaron ta ce tuni ta kaddamar da bincike domin gano musababbin wannan hadari, tare da bayyana juyayi dangane da faruwar lamarin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp