Home DUNIYA Ma’aikatar Tsaron Jamhuriyyar Nijar ta tabbatar da Mutuwar Mutane 3 sakamakon Hadarin...

Ma’aikatar Tsaron Jamhuriyyar Nijar ta tabbatar da Mutuwar Mutane 3 sakamakon Hadarin Jirgin Yaki

Wani jirgin soji mai saukar angulu kirar Mi-17, ya yi hadadi a filin sauka da tashin jiragen saman birnin Yamai da ke jamhuriyar Nijar, inda mutane uku da ke cikinsa suka rasa rayukansu nan take.

Ma’aikatar tsaron kasar ta ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 10 da mintuna 40 na safe.

Wata sanarwa da ma’aikatar da ma’aikatar tsaron kasar ta fitar a tsakiyar ranar litinin, ta ce jirgin ya yi hadari ne lokacin da yake sauka, bayan dawowa daga atisayen bayar da horo, kuma wadanda suka rasa rayukansu sun hadar da babban hafsan soji daya, da karamin hafsa daya sai kuma wanda ke horas da su dan asalin wata kasa ta kerare.

Ma’aikatar tsaron ta ce tuni ta kaddamar da bincike domin gano musababbin wannan hadari, tare da bayyana juyayi dangane da faruwar lamarin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp