Home General Gwamnatin Jihar Kano zata Kaddamar da Sabuwar Tashar wutar Lantarki a jihar

Gwamnatin Jihar Kano zata Kaddamar da Sabuwar Tashar wutar Lantarki a jihar

Gwamnatin Jihar Kano a Arewacin Najeriya ta ce nan da makwanni 6 za a kammala aikin tashar samar da wutar lantarki ta Tiga mai karfin mega watt 10
Gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje ya ba da tabbacin ne lokacin ziyarar ganin yadda aikin tashar samar da wutar lantarki na Tiga da na samar da ruwa da ke Tamburawa yake gudana.
Cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran gwamnan Malam Abba Anwar ya fitar a jihar Kano, ta ce tashar samar da wutar lantarkin a matakin gwaji kafin kaddamarwa.
Gwamnan ya kuma yabawa kamfanin samar da hasken wutar lantarki mallakin jihar KHEDCO da kamfanin da aka baiwa kwangilar aiki da kuma sauran masu ruwa da tsaki.
A cewar gwamnan na da makwanni kadan wutar lantarkin na Tiga za a jona shi da tashar samar da ruwa ta Tamburawa , yana mai bada tabbacin cewa zai yi iyakar kokari dan ganin ya bar tarihi a dukkanin bangarorin ciyar da al’umma gaba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp