Home General Gwamnatin Jihar Kano zata Kaddamar da Sabuwar Tashar wutar Lantarki a jihar

Gwamnatin Jihar Kano zata Kaddamar da Sabuwar Tashar wutar Lantarki a jihar

Gwamnatin Jihar Kano a Arewacin Najeriya ta ce nan da makwanni 6 za a kammala aikin tashar samar da wutar lantarki ta Tiga mai karfin mega watt 10
Gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje ya ba da tabbacin ne lokacin ziyarar ganin yadda aikin tashar samar da wutar lantarki na Tiga da na samar da ruwa da ke Tamburawa yake gudana.
Cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran gwamnan Malam Abba Anwar ya fitar a jihar Kano, ta ce tashar samar da wutar lantarkin a matakin gwaji kafin kaddamarwa.
Gwamnan ya kuma yabawa kamfanin samar da hasken wutar lantarki mallakin jihar KHEDCO da kamfanin da aka baiwa kwangilar aiki da kuma sauran masu ruwa da tsaki.
A cewar gwamnan na da makwanni kadan wutar lantarkin na Tiga za a jona shi da tashar samar da ruwa ta Tamburawa , yana mai bada tabbacin cewa zai yi iyakar kokari dan ganin ya bar tarihi a dukkanin bangarorin ciyar da al’umma gaba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp