Mutum 8 Sun Mutu a rikicin kabilanci a Sudan

Jami’an agaji a yankin Darfur na ƙasar Sudan sun ce akalla mutane takwas ne suka mutu a rikicin da ya ɓarke a cikin dare tsakanin wasu al’ummomin da ke zaman doya da manja.

Da farko dai an fara harbe-harbe ne a garin Zalingei, daga bisani ‘yan kabilar Rizeigat ta Larabawa, da suka kai hari wani sansanin ‘yan gudun hijira na ‘yan kabilar Fur, a kan babura.

Ɓarkewar tashe-tashen hankula sun karu tun bayan janyewar tawagar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya a bara.

Har yanzu dai yankin na Darfur bai farfaɗo ba daga yaƙin da ya sha fama da shi tun kusan shekaru ashirin da suka gabata, wanda ya raba sama da mutane miliyan biyu da gidajensu.

Ana zargin da sa hannun wasu mayakan sa kai da ke samun goyon bayan gwamnati a wasu hare-haren da ake kaiwa.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 23 minutes 33 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 4 minutes 58 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com