Wasu Sabbin Hare-Haren ‘Yan Bindiga a Jihohin Sokoto da Katsina sun yi sandiyyar Mutuwar Mutane 13 tare da garkuwa da 73

‘Yan bindiga sun sake hallaka mutane 14, tare da yin garkuwa da 18 a jihohin Sokoto da Katsina dake arewa maso yammacin Nijeriya.

A gabashin jihar Sokoto , an hallaka mutane 13 tare da yin garkuwa da 73 wanda suka hadar da mata da kananan yara.

Hare-haren ya auku a kauyuka mabanbamta, da suka hadar da sabon birni, gada da kuma yankunan karamar hukumar Goronyo.

Jaridar daily ta ruwato cewa an dukkan hare-haren an kai su ne a lokaci gusa ranar litinin din makoon daya gabata.

Da yake tattaunawa da jaridar wani mai rike da sarautar gargajiya a sabon birin, wanda ya bukaci a sakaye sunan sa, ya ce kauyuka 3 mayakan suka kaiwa hari a karamar hukumar sa inda suka hallaka mutane 11.

Kauyukan sun hadar da gatawa da Dangari inda mutane 6 suka mutu, 2 a gatawa 3 kuma a kurawa.

Shugaban jami’an sa kai na Vijilanti a sabonda birni, Musa Muhammad da Dan Majalisa ma wakiltar sabon birnin a zauren majalisar wakilai Mustapha Boza, dake wakiltar Sabon birni ta kudu su bayyana cewa dukkan  mutanen an halaka su ne a gona ranar litinin da karfe 5 na yamma.

Boza yace sun kuma yi garkuwa da mutane da dama yayi da suka kai harin.

Haka kuma shugaban karamar hukumar Goronyo, Abdulwahab Goronyo, wand aya koka bisa harin yace maharani sun hallaka mutane 23, yayin da suka yi garkuwa da sauran a garuruwan shinkafi da  kagara a ranar litinin din data gabata.

shima Dan majalisa mai wakiltar mazabar Gada ta gabas a zauren majalisar jiha, Kabiru dauda, ya bayyana cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane sama da 50 da suka hadar da mata da kananan yara a ranar litinin a yankin.

“bazan iya fada maka takamaiman adadin mutanen da aka sace ba, amma da yawan mutanen mun sun samin raukana, amma dai suka samun kulawar likitoci a asibitocin daban-daban. Kamar yadda ya bayyana.

Dauda ya hakikance cewa duk da korafe-korafen da Al’ummar ke yi bisa harin rashin  tsaron da suke ciki, kawo yanzu babu wani matakin da aka dauka domin magance matsalar ba.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 42 minutes 12 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 23 minutes 37 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com