Home Labarai Hatsarin jirgin ƙasa ya kashe aƙalla mutum uku a Legas

Hatsarin jirgin ƙasa ya kashe aƙalla mutum uku a Legas

An tabbatar da mutuwar aƙalla mutum uku, yayin da wasu da dama suka samu rauni lokacin da jirgin ƙasa ya buge wata motar bas da safiyar Alhamis a yankin Ikeja da ke jihar Legas.

Shugaban Hukumar agajin gaggauwa ta ƙasa (NEMA), na yankin kudu maso yammacin Najeriya, Ibrahim Farinloye shi ne ya tabbatar da lamarin.

A baya jami’in ya ce mutum biyu ne, sai dai daga bisani ya ce yawan waɗanda suka mutu ɗin ya ƙaru zuwa uku.

Ya ce “mata biyu ma’aikatan gwamnatin jiha da wani namiji ne suka rasu.”

Motar bas ɗin wadda ta gwamnatin jiha ce na ƙoƙarin tsallaka hanyar jirgin ƙasa ta PWD/Sogunle ne a lokacin da jirgin, wanda ya fito daga Abeokuta zuwa cikin birnin Legas ya yi awon-gaba da ita.

Mai magana da yawun Hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Legas, Adebayo Taofiq shi ma ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ana dai ci gaba da aikin ceto, domin tabbatar da cewa babu sauran wanda abin ya rutsa da shi a maƙale.

Mutane sun rinƙa yaɗa hotunan da suka fito daga wurin da haɗarin ya faru.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp