Mayakan kungiyar ISWAP sun kashe masunta 37 a jihar Borno

Rahotannin na bayyana cewa mayakan kungiyar ISWAP sun kashe masunta 37 a jihar Borno ta arewa maso gabashin Najeriya yayin wani hari da suka kai kansu lokacin da suke tsaka da aiki.

Jagoran mayakan sa kai na jihar Borno Babakura Kolo ya shaidawa AFP cewa ‘yan ta’addan sun farmaki Masuntan ne da ke aikin kamun kifi a wajen kauyen Guggo mai tazarar kilomita 18 daga garin Dikwa tare da kasha mutane 37 ta hanyar harbinsu da kuma jefa gawarwakinsu a ruwa.

Majiyoyi daga yankin sun tabbatarwa kamfanin dillancin labarai na AFP yau alhamis cewa a baya-bayan nan mayakan na ISWAP da takwarorinsu Boko Haram sun tsananta kai hare-hare kan kauyukan jihar ta Borno don satar kayakin abinci.

Mayakan sa kai da ke taimakawa dakarun Sojin Najeriya wajen dakile hare-haren ‘yan ta’adda a yankin sun ce babu tabbaci kan tsagin da ya kai harin na jiya sai dai an tsamo gawarwakin Masuntan 37 a cikin ruwa jiya laraba.

A cewar mayakan, ana ci gaba da laluben gawarwaki a cikin ruwan da kuma cikin dazuka lura da yadda har yanzu aka gaza gano wasu daga cikin Masuntan da suka yi batan dabo.

Rahotanni sun ce mayakan kungiyoyin ‘yan ta’addan na ISWAP da Boko Haram na zargin mazauna kauyukan ko kuma masuntan da sauran manoma da aikin leken asiri ga Sojin Najeriya dalilin da ya sanya kai musu hari.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 15 minutes 22 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 56 minutes 47 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com