Home Labarai Mutum 5 sun kone kurmus a wani hadarin mota a Badagry zuwa...

Mutum 5 sun kone kurmus a wani hadarin mota a Badagry zuwa Seme

Wani hadarin mota akan babbar hanyar badagry zuwa Seme a jihar legas yayi sanadiyar konewar mutane biyar tare da raunata da dama a ranar Alhamis.

Kwamandan hadakar jami’an hukumar kiyaye haddura ta dake badagry Mista Sulaiman Taiwo ya tabbatar da faruwar hakan ga kamfanin dillacin labarai na Nijeriya (NAN).

Inda yace hadarin yace hadarin ya auku ne a kauyen Akoro, dake daura da babbar hanyar badagry zuwa semi a jihar ta legasa dake kudu masu yammacin Nijeriya.

Hadarin ya auke ne tsakanin wata mota mai kirar Honda Pilot SUV dake da lamba LSR 772 HE da wani babur da aka kasa gane lamabr dake jikin sa.

Taiwo yace direban motar na gudun wuce sa’a ne, inda ya kasa sarrafa motar abinda ya sanya shi dukan mai babur din dake dauke da man fetur. Wannan ne ya sanya tashin wuta a yayi tawo mu gama tsakanin motar da babur din.

Mutum 3 da suka tsira da raunika a jikkunan su na karbar kulawa a babban asibitin Badagry, haka kuma gawarwakin mutum 5 kuma an kai su dakin ajiyar gawa na asibitin” a cewar sa.

Taiwo ya kara da cewa daukin gaggawa da jami’an kwastom dana kasha gobara gami da jami’an tsaro na civil defence da ‘yan sanda sukayi ya taimaka wajen dawo da wurin da lamarin ya auku yadda ya kamata.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp