Home Labarai Mutum 5 sun kone kurmus a wani hadarin mota a Badagry zuwa...

Mutum 5 sun kone kurmus a wani hadarin mota a Badagry zuwa Seme

Wani hadarin mota akan babbar hanyar badagry zuwa Seme a jihar legas yayi sanadiyar konewar mutane biyar tare da raunata da dama a ranar Alhamis.

Kwamandan hadakar jami’an hukumar kiyaye haddura ta dake badagry Mista Sulaiman Taiwo ya tabbatar da faruwar hakan ga kamfanin dillacin labarai na Nijeriya (NAN).

Inda yace hadarin yace hadarin ya auku ne a kauyen Akoro, dake daura da babbar hanyar badagry zuwa semi a jihar ta legasa dake kudu masu yammacin Nijeriya.

Hadarin ya auke ne tsakanin wata mota mai kirar Honda Pilot SUV dake da lamba LSR 772 HE da wani babur da aka kasa gane lamabr dake jikin sa.

Taiwo yace direban motar na gudun wuce sa’a ne, inda ya kasa sarrafa motar abinda ya sanya shi dukan mai babur din dake dauke da man fetur. Wannan ne ya sanya tashin wuta a yayi tawo mu gama tsakanin motar da babur din.

Mutum 3 da suka tsira da raunika a jikkunan su na karbar kulawa a babban asibitin Badagry, haka kuma gawarwakin mutum 5 kuma an kai su dakin ajiyar gawa na asibitin” a cewar sa.

Taiwo ya kara da cewa daukin gaggawa da jami’an kwastom dana kasha gobara gami da jami’an tsaro na civil defence da ‘yan sanda sukayi ya taimaka wajen dawo da wurin da lamarin ya auku yadda ya kamata.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp