Home Labarai Mutum 5 sun kone kurmus a wani hadarin mota a Badagry zuwa...

Mutum 5 sun kone kurmus a wani hadarin mota a Badagry zuwa Seme

Wani hadarin mota akan babbar hanyar badagry zuwa Seme a jihar legas yayi sanadiyar konewar mutane biyar tare da raunata da dama a ranar Alhamis.

Kwamandan hadakar jami’an hukumar kiyaye haddura ta dake badagry Mista Sulaiman Taiwo ya tabbatar da faruwar hakan ga kamfanin dillacin labarai na Nijeriya (NAN).

Inda yace hadarin yace hadarin ya auku ne a kauyen Akoro, dake daura da babbar hanyar badagry zuwa semi a jihar ta legasa dake kudu masu yammacin Nijeriya.

Hadarin ya auke ne tsakanin wata mota mai kirar Honda Pilot SUV dake da lamba LSR 772 HE da wani babur da aka kasa gane lamabr dake jikin sa.

Taiwo yace direban motar na gudun wuce sa’a ne, inda ya kasa sarrafa motar abinda ya sanya shi dukan mai babur din dake dauke da man fetur. Wannan ne ya sanya tashin wuta a yayi tawo mu gama tsakanin motar da babur din.

Mutum 3 da suka tsira da raunika a jikkunan su na karbar kulawa a babban asibitin Badagry, haka kuma gawarwakin mutum 5 kuma an kai su dakin ajiyar gawa na asibitin” a cewar sa.

Taiwo ya kara da cewa daukin gaggawa da jami’an kwastom dana kasha gobara gami da jami’an tsaro na civil defence da ‘yan sanda sukayi ya taimaka wajen dawo da wurin da lamarin ya auku yadda ya kamata.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp