Home Labarai Mayakan kungiyar ISWAP sun kashe masunta 37 a jihar Borno

Mayakan kungiyar ISWAP sun kashe masunta 37 a jihar Borno

Rahotannin na bayyana cewa mayakan kungiyar ISWAP sun kashe masunta 37 a jihar Borno ta arewa maso gabashin Najeriya yayin wani hari da suka kai kansu lokacin da suke tsaka da aiki.

Jagoran mayakan sa kai na jihar Borno Babakura Kolo ya shaidawa AFP cewa ‘yan ta’addan sun farmaki Masuntan ne da ke aikin kamun kifi a wajen kauyen Guggo mai tazarar kilomita 18 daga garin Dikwa tare da kasha mutane 37 ta hanyar harbinsu da kuma jefa gawarwakinsu a ruwa.

Majiyoyi daga yankin sun tabbatarwa kamfanin dillancin labarai na AFP yau alhamis cewa a baya-bayan nan mayakan na ISWAP da takwarorinsu Boko Haram sun tsananta kai hare-hare kan kauyukan jihar ta Borno don satar kayakin abinci.

Mayakan sa kai da ke taimakawa dakarun Sojin Najeriya wajen dakile hare-haren ‘yan ta’adda a yankin sun ce babu tabbaci kan tsagin da ya kai harin na jiya sai dai an tsamo gawarwakin Masuntan 37 a cikin ruwa jiya laraba.

A cewar mayakan, ana ci gaba da laluben gawarwaki a cikin ruwan da kuma cikin dazuka lura da yadda har yanzu aka gaza gano wasu daga cikin Masuntan da suka yi batan dabo.

Rahotanni sun ce mayakan kungiyoyin ‘yan ta’addan na ISWAP da Boko Haram na zargin mazauna kauyukan ko kuma masuntan da sauran manoma da aikin leken asiri ga Sojin Najeriya dalilin da ya sanya kai musu hari.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp