Home Labarai Mayakan kungiyar ISWAP sun kashe masunta 37 a jihar Borno

Mayakan kungiyar ISWAP sun kashe masunta 37 a jihar Borno

Rahotannin na bayyana cewa mayakan kungiyar ISWAP sun kashe masunta 37 a jihar Borno ta arewa maso gabashin Najeriya yayin wani hari da suka kai kansu lokacin da suke tsaka da aiki.

Jagoran mayakan sa kai na jihar Borno Babakura Kolo ya shaidawa AFP cewa ‘yan ta’addan sun farmaki Masuntan ne da ke aikin kamun kifi a wajen kauyen Guggo mai tazarar kilomita 18 daga garin Dikwa tare da kasha mutane 37 ta hanyar harbinsu da kuma jefa gawarwakinsu a ruwa.

Majiyoyi daga yankin sun tabbatarwa kamfanin dillancin labarai na AFP yau alhamis cewa a baya-bayan nan mayakan na ISWAP da takwarorinsu Boko Haram sun tsananta kai hare-hare kan kauyukan jihar ta Borno don satar kayakin abinci.

Mayakan sa kai da ke taimakawa dakarun Sojin Najeriya wajen dakile hare-haren ‘yan ta’adda a yankin sun ce babu tabbaci kan tsagin da ya kai harin na jiya sai dai an tsamo gawarwakin Masuntan 37 a cikin ruwa jiya laraba.

A cewar mayakan, ana ci gaba da laluben gawarwaki a cikin ruwan da kuma cikin dazuka lura da yadda har yanzu aka gaza gano wasu daga cikin Masuntan da suka yi batan dabo.

Rahotanni sun ce mayakan kungiyoyin ‘yan ta’addan na ISWAP da Boko Haram na zargin mazauna kauyukan ko kuma masuntan da sauran manoma da aikin leken asiri ga Sojin Najeriya dalilin da ya sanya kai musu hari.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp