Gwamnatin Buhari na shirin cire tallafin Man Fetur

Gwamnatin Najeriya ta ce ta na shirin kammala cire tallafin man fetur kafin mika mulki ga sabuwar gwamnati a ranar 29 ga watan Mayun wannan shekara.

Ministar kudi da tsare tsaren kasar Zainab Shamsuna Ahmed ta bayyana shirin a Abuja, inda ta ke cewa shirin cire tallafin shi ne wanda jama’a basa so amma kuma ya zama wajibi, a dai dai lokacin da akasarin ‘yan Najeriya suka yarda cewar tallafin baya taimakon talaka.

Ahmed ta ce sun samu umurnin cire tallafin nan da watan Yuni na wannan shekara kamar yadda majalisa ta amince da shi a cikin kasafin kudin wannan shekara, kuma za su aiwatar da shi domin bai wa kasuwa damar samar da farashin a koda yaushe.

Ministar ta ce idan an cire tallafin, zai ba iwa ‘yan kasuwa da masu zuba jari damar shiga harkokin kasuwancin man da kuma samar da shi ga jama’a.

Zainab Ahmed ta ce kawo karshen zuba tallafin man zai bai wa gwamnati damar karkata kudin da ake sanyawa zuwa bangarori da dama da suka hada da inganta asibitoci da makarantu da kuma samar da kayan more rayuwa.

Ministar ta bukaci ‘yan Najeriya da su goyawa gwamnatin baya wajen ganin an kawo karshen wannan tallafi wanda ke amfana wasu mutane ‘yan kadan.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 38 minutes 22 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 19 minutes 47 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com