Home Labarai NBC ta sanyawa wasu kafafen yada labarai 25 takunkumi sakamakon karya dokoki

NBC ta sanyawa wasu kafafen yada labarai 25 takunkumi sakamakon karya dokoki

Hukumar dake lura da kafafen yada labarai ta Najeriya NBC ta sanyawa wasu kafafen yada labarai 25 takunkumi sakamakon karya dokokin hukumar a lokacin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya.

Daraktan hukumar na kasa Balarabe Shehu Illele ne ya bayyana hakan a ranar Laraba yayin da yake zantawa da manema labarai, inda ya kara da cewa hukumar ta kuma baiwa wasu kafafen yada labarai 16 gargadi domin su gyara ayyukansu.

Ya kara da cewa wasu daga cikin wadannan kafafen yada labaran sun baiwa baki da masu fashin baki har ma da masu kiran waya a yayin shirye-shirye damar furta wasu kalmomi mara sa da dadi ba tare da yi musu linzami ba.

Balarabe Illela ya kuma bukaci sauran kafafen yada labaran kasar da su mayar da hankali wajen sanya kwarewa da kuma bin doka da oda yayin gudanar da ayyukansu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp