Home Labarai NBC ta sanyawa wasu kafafen yada labarai 25 takunkumi sakamakon karya dokoki

NBC ta sanyawa wasu kafafen yada labarai 25 takunkumi sakamakon karya dokoki

Hukumar dake lura da kafafen yada labarai ta Najeriya NBC ta sanyawa wasu kafafen yada labarai 25 takunkumi sakamakon karya dokokin hukumar a lokacin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya.

Daraktan hukumar na kasa Balarabe Shehu Illele ne ya bayyana hakan a ranar Laraba yayin da yake zantawa da manema labarai, inda ya kara da cewa hukumar ta kuma baiwa wasu kafafen yada labarai 16 gargadi domin su gyara ayyukansu.

Ya kara da cewa wasu daga cikin wadannan kafafen yada labaran sun baiwa baki da masu fashin baki har ma da masu kiran waya a yayin shirye-shirye damar furta wasu kalmomi mara sa da dadi ba tare da yi musu linzami ba.

Balarabe Illela ya kuma bukaci sauran kafafen yada labaran kasar da su mayar da hankali wajen sanya kwarewa da kuma bin doka da oda yayin gudanar da ayyukansu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp