Home Labarai An dage lokacin kidaya a Nijeriya

An dage lokacin kidaya a Nijeriya

Gwamnatin Najeriya ta sanar da jinkirta lokacin gudanar da Shirin kidayar jama’ar kasar da aka shirya yi a wannan wata na Maris zuwa watan Mayu mai zuwa.

Ministan yada labarai Lai Mohammed ya sanar da haka bayan wani taron majalisar ministoci a fadar shugaban kasa da aka gudanar ranar laraba.

Mohammed ya danganta dage shirin da jinkirta zaben gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi da hukumar zabe tayi, abinda ya jirkita shirin hukumar kidayar.

Ministan yace majalisar ministocin Najeriya ta amince da bukatar hukumar na karbar kudin da ya kai naira biliyan 2 da miliyan 800 domin sayen na’urorin zamanin da za’ayi amfani da su wajen gudanar da aikin.

Rahotanni sun ce za’a gudanar da kidayar ce daga ranakun 3 zuwa 7 ga watan Mayu kamar yadda aka baiwa shugaban kasa Muhammadu Buhari shawara.

Kidayar jama’a na daya daga cikin ayyuka masu sarkakiya a Najeriya saboda banbance banbancen dake tsakanin al’umma wadanda ake zargi da aringizon jama’a duk lokacin gudanar da irin wannan kidayar. Rabon Najeriya da gudanar da kidayar jama’a tun daga shekarar 2006.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp