Home Labarai An dage lokacin kidaya a Nijeriya

An dage lokacin kidaya a Nijeriya

Gwamnatin Najeriya ta sanar da jinkirta lokacin gudanar da Shirin kidayar jama’ar kasar da aka shirya yi a wannan wata na Maris zuwa watan Mayu mai zuwa.

Ministan yada labarai Lai Mohammed ya sanar da haka bayan wani taron majalisar ministoci a fadar shugaban kasa da aka gudanar ranar laraba.

Mohammed ya danganta dage shirin da jinkirta zaben gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi da hukumar zabe tayi, abinda ya jirkita shirin hukumar kidayar.

Ministan yace majalisar ministocin Najeriya ta amince da bukatar hukumar na karbar kudin da ya kai naira biliyan 2 da miliyan 800 domin sayen na’urorin zamanin da za’ayi amfani da su wajen gudanar da aikin.

Rahotanni sun ce za’a gudanar da kidayar ce daga ranakun 3 zuwa 7 ga watan Mayu kamar yadda aka baiwa shugaban kasa Muhammadu Buhari shawara.

Kidayar jama’a na daya daga cikin ayyuka masu sarkakiya a Najeriya saboda banbance banbancen dake tsakanin al’umma wadanda ake zargi da aringizon jama’a duk lokacin gudanar da irin wannan kidayar. Rabon Najeriya da gudanar da kidayar jama’a tun daga shekarar 2006.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp