Home Labarai NDLEA ta tabbatar da gyara shafinta na daukar aiki

NDLEA ta tabbatar da gyara shafinta na daukar aiki

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta NDLEA ta tabbatawar wa ‘yan Nijeriya dake neman aiki a hukumar cewa ta shawo kan matsalar da ake fuskanta a shafinta na daukar aiki da nufin ganin an sami mafita daga yanzu zuwa ko wanne lokaci.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran hukumar Femi babafemi ya fitar, mai dauke da kwanan wata 15 ga watan Maris 2023. Inda yace sa’oi kadan da bude shafin a ranar lahadi 12 ga wata Maris, ya fara samun tangarda sakamakon yadda mutane sama da dubu 200 ke kokarin cike takardar samun gurbin aiki a hukumar.

Domin warware wannan matsalar hukumar a ranar talata 14 ga watan Maris ta inganta shafin domin daukar dimbin masu bukatar samun gurbin aiki a hakumar bayan da sama da mutane 53,170 suka nasara shiga tashin.

A halin yanzu, shafin yana aiki yadda ya kamata. Don haka hukumar na amfani da wannan dama wajen neman afuwar wadanda suka bibiyi shafin bisa tsaikon da suka samu da su kara hakuri.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp